HausaTv:
2025-06-19@19:05:51 GMT

 Zimbabwe: Za A Yanka Giwaye 50 A Rabawa Mutanen Karkara Namansu

Published: 9th, June 2025 GMT

Tare da cewa giwaye suna cikin dabbobin da masu yawon bude ido suke son gani, said ai gwamantin kasar Zimbabwe ta yanke hukunci yanka 50 daga cikinsu domin rabawa mutanen karkara namansu.

Wannan matakin na gwamnatin Zimbabwe ya zo ne saboda yadda giwayen suke kara yawa sosai a cikin shekarun bayannan.

Haka nan kuma wuraren da ake killace su, sun yi kadan.

Majiyar dake kula da gandun dajin kasar ta ce; adadin giwayen ya rubanya har sau uku, wannan ne ya sa mahukuntar kasar su ka yanke shawarar yanka 50 daga cikinsu saboda a rabawa mutanen karkara.

A baya gwamnatin na Zimbabwe ya yi kokarin warware matsalar karuwar dabbobin ta hanyar sauya musu gandun daji da wuraren da aka killace ta hanyar lika musu na’urar da take bibiyar kai da komowarsu ta       ( GPS). Haka nan kuma tana amfani da wannan fasahar wajen gargadin mutanen Karkare idan wata dabba ta karaci kauyukansu.

A shekarar da ta gabata kasar ta Zimbawe ta kashe giwaye 200 saboda farin da aka fuskanta wanda ya sa aka sami karancin abinci a kasar.

A wanann shekarar dai adadin giwayen da za a yanka ba su wuce 50 ba, zuwa yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin ta shirya tsaf wajen aiwatar da soke haraji da kashi 100 bisa 100 a kan kayayyakin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar jakadanci da kasar ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a fannin raya tattalin arziki.

 

A yau, wani jami’in ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ya gabatar da wani batu da ya dace da hakan. Inda ya bayyana cewa, a mataki na gaba, ma’aikatar kasuwanci za ta yi aiki tare da sassan da abin ya shafa, wajen inganta kulla yarjejeniyar hadin gwiwa ta fuskar tattalin arziki don samun ci gaba na bai-daya tare da kasashen Afirka bisa ka’idojin tuntubar juna da samun moriyar juna dai-dai-wa-daida. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev