HausaTv:
2025-06-09@15:35:06 GMT

 Zimbabwe: Za A Yanka Giwaye 50 A Rabawa Mutanen Karkara Namansu

Published: 9th, June 2025 GMT

Tare da cewa giwaye suna cikin dabbobin da masu yawon bude ido suke son gani, said ai gwamantin kasar Zimbabwe ta yanke hukunci yanka 50 daga cikinsu domin rabawa mutanen karkara namansu.

Wannan matakin na gwamnatin Zimbabwe ya zo ne saboda yadda giwayen suke kara yawa sosai a cikin shekarun bayannan.

Haka nan kuma wuraren da ake killace su, sun yi kadan.

Majiyar dake kula da gandun dajin kasar ta ce; adadin giwayen ya rubanya har sau uku, wannan ne ya sa mahukuntar kasar su ka yanke shawarar yanka 50 daga cikinsu saboda a rabawa mutanen karkara.

A baya gwamnatin na Zimbabwe ya yi kokarin warware matsalar karuwar dabbobin ta hanyar sauya musu gandun daji da wuraren da aka killace ta hanyar lika musu na’urar da take bibiyar kai da komowarsu ta       ( GPS). Haka nan kuma tana amfani da wannan fasahar wajen gargadin mutanen Karkare idan wata dabba ta karaci kauyukansu.

A shekarar da ta gabata kasar ta Zimbawe ta kashe giwaye 200 saboda farin da aka fuskanta wanda ya sa aka sami karancin abinci a kasar.

A wanann shekarar dai adadin giwayen da za a yanka ba su wuce 50 ba, zuwa yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Kasar Rwanda Ta Fice Daga Cikin Kungiyar Tattalin Arziki Ta Tsakiyar  Afirka

A daidai lokacin da kungiyar kasashen  tsakiyar Afirka ta tattalin arziki        ( ECCAS) take yin taro, kasar Rwanda ta sanar da ficewa daga cikinta.

Bayanin da gwamnatin kasar ta Rwanda ta fitar ya kunshi cewa; Kasar Rwanda tana nuna takaicinta akan yadda kasar DRC take amfani da kungiyar tattalin arziki ta  tsakiyar Afirka a matsayin wani makamin a hannunta.”

Bayanin gwamnatin ta Rwanda ya kara da cewa: Yadda DRC take amfani da wannan kungiyar ya sake fitowa fili a yayin taron kungiyar karo na 26 a Malabo, ta yadda aka kau da kai akan hakkin Rwanda na shugabancin karba-karba,kamar yadda yake a cikin doka ta shida ta kundin kungiyar. Hakan kuma ya faru ne sanadiyyar shiftar DRC ga kungiyar.”

A yayin da aka shirya cewa a shekara mai zuwa kasar ta Rwanda za ta karfi shugabancin kungiyar, jami’an kasar DRC sun ce, ba za su sami halartar taron da za a yi a kasar ta Rwanda ba.

Kasashen biyu dai suna zaman tsami bisa zargin da Kinshasa take yi wa  Kigali na cewa tana goyon bayan kungiyar ‘yan tawaye ta M23.

Yanzu dai kungiyar ta ECCAS tana da mamabobi 11 bayan ficewar kasar Rwanda. Kasashen su ne: Angola, Burundi, Cameroon, Afirka Ta Tsakiya,c, Congo, Gabon, Equatorial Guinea,  Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, Rwanda, Sao Tome, sai  tsibirin Principe da  Chad.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kasar Rwanda Ta Fice Daga Cikin Kungiyar Tattalin Arziki Ta Tsakiyar  Afirka
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
  • Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000
  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran
  • Rundunar Sojin Mamayar Isra’ila Ta Yi Furuci Da Karancin Sojoji Saboda Raguwarsu Sanadiyyar Mutuwa  Ko Rashin Lafiya
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
  • Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
  • Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom