Aminiya:
2025-06-09@11:19:10 GMT

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba

Published: 9th, June 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fara sana’a na cikin manyan jerin kalubalen da ’ƴan Najeriya suke fuskanta sakamakon wasu dalilai wadanda suka hada da rashin ilimi, ko Rashin wanda zai ba su shawara ko kuma, uwa uba, rashin jari.

 

Wasu bayanai da Hukumar Ƙididdiga Ta Kasa – NBS – ta fitar sun nuna cewa fiye da kashi 40 cikin 100 na matasan Najeriya suna sha’awar fara sana’a, amma sun kasa saboda rashin jari.

Haka kuma, wani bincike da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya gudanar ya nuna cewa kashi 65 cikin 100 na matasa masu so su fara kasuwanci suna fuskantar babbar tangarda wajen samun jari daga bankuna ko hukumomin gwamnati.

Shin ko akwai wata hanya da matasa za su bi su fara sana’a ko da ba su da jari?

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah

Wannan shine batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dabarun kasuwanci jari

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

A masana’antar Nollywood dake Kudancin Nijeriya, manyan masu kudinsu, sarakuna, hukumomi da gwamnatoci na iyakar kokarinsu wajen ganin masana’antar ta cigaba, ta hanyoyi daban daban da suka hada da kayan aiki, wajen daukar fim, fadada ilimi, tallace tallace da sauran tallafi da masana’antar ke bukata, a wasu lokutan ma akan daukesu har kasashen Turai wajen koyon aiki da kuma tallata hajarsu ga manyan dillalan fim a Duniya wanda ta wannan hanyar sai su samu manyan kudade.

T Y ya cigaba da cewa idan ana maganar masana’antar Kannywood ba haka abin yake ba, domin kuwa a nan yankin sai mai shirya fim ya nemi gida ko kamfanin da zai shirya fim din sa ya rasa, hakan zai sa ya je ya dauki Hotel ko wani gidan haya domin gudanar da aikinsa wanda yace ta haka ne zakaga fina finai suna kamanceceniya da juna saboda kusan komai da komai a waje daya akayi su sakamakon rashin wurare.

Mu a nan arewacin Nijeriya har yanzu ba a daukemu a matsayin wasu da zasu iya kawo cigaba kokuma su samar da aiyuka ga matasa ba, shi yasa ba duk taimako ake mana ba saboda a nasu tunanin babu wani abin cigaba da zamu iya kawowa, yanzu ga misali wanda yafi kowane mutum dukiya a nahiyar Afirika dan arewa ne kuma bahaushe, amma idan yanzu ana son ayi fim wanda za a taka rawar babban mutum kamar Dangote ba lallai bane hakan ta faru.

Saboda ba za a samu isassun manyan gidaje ko manyan motoci da za ayi amfani dasu a fim din ba duk da cewa akwai su da dama, don haka ina kira ga manyan masu kudinmu, mahukuntanmu, sarakuna da gwamnatocinmu su yi kokarin taimakawa wannan masana’antar ta Kannywood da ake shirya fina finai da harshen Hausa ta kowane fanni, hakan zai sa muyi gogayya da takwarorinmu na gida da ma na kasashen waje inji TY Shaba.

Daga karshe ya bukaci matasa da su kasance masu biyayya da hakuri, da kuma jajircewa wajen ganin burikansu sun cika, yace dole ne sai an sha wuya akan sha dadi, kuma duk wanda suka gani a cikin masana’antar Kannywood babu wanda ya shigo a matsayin mai kudi, kowa a talaka ya fara kafin ya zama abinda ya zama, don haka kuma idan kukayi hakuri komai zai zo ya wuce ba tareda wata tangarda ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa
  • Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah
  • Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
  • Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah
  • Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja
  • Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
  • Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
  • Adadin ‘Yan Jaridar Falasdinu Da Suka Yi Shahada Sun Karu Zuwa 226 Tun Bayan Fara Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC