HausaTv:
2025-11-03@02:08:07 GMT

Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji

Published: 11th, June 2025 GMT

Sojojin HKI sun kai hari akan Falasdinawan da su ka yi cincirindo domin karbar abinci da hakan ya yi sanadiyyar shahadar da dama daga cikinsu.

Tun da safiyar yau Laraba ne dai sojojin HKI su ka rika kai hare-hare akan cibiyoyin cibiyoyin raba agaji wadanda dama suna a karkashin kulawar su kansu ‘yan sahayoniyar da kuma Amurka.

Har ila yau hare-haren sun shafi gidajen fararen hula a cikin wasu unguwanni na zirin Gaza.

Majiyar Asibitin “Audah” ta sanar da cewa an kai shahida 4 da kuma wadanda su ka jikkata sanadiyyar hare-haren na sojojin mamaya a wurin raba kayan agaji dake kan titin “Salahuddin” a tsakiyar zirin Gaza.

A arewacin yankin Gaza kuwa wasu samarin Falasdinawa 4 sun yi shahada bayan da jiragen yakin HKI su ka kai hari a kusa da makarantar “Usamatu Bin Zayd” dake yankin Safdhawi.

Wasu jiragen yakin na ‘yan mamaya sun kai wasu hare-haren a unguwar “Basrah’ dake birnin Gaza. Ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko yin shahada.

A kusa da mashigar ‘al-Buraij’ ma sojojin mamayar sun kai hari da jirgin sama maras matuki akan mutane da suka yi cirko-cirko suna tsumayen kayan agaji.

Wasu wuraren da aka sami shahidai sun hada da sansanin ‘yan hijira na “Nusairat’ da “Muwasi” a Khan-Yunus, sai kuma  “Badhnus-samin”.

Tun a makwannin da su ka gabata ne dai MDD ta sanar da cewa ba za ta shiga cikin tsarin dake karkashin HKI da Amurka ba, na raba kayan agaji, saboda manufarsa korar Falasdinawa daga gidajensu. Ita kuwa kungiyar Hamas ta ce, wuraren na rabon agaji sun zama tarko kisa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A cewarsa, ta hanyar wadannan shirye-shirye, kasar Sin ta nuna goyon baya mai dorewa ga kasashe masu tasowa kuma tana ba da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban duniya a karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa