Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
Published: 11th, June 2025 GMT
Sojojin HKI sun kai hari akan Falasdinawan da su ka yi cincirindo domin karbar abinci da hakan ya yi sanadiyyar shahadar da dama daga cikinsu.
Tun da safiyar yau Laraba ne dai sojojin HKI su ka rika kai hare-hare akan cibiyoyin cibiyoyin raba agaji wadanda dama suna a karkashin kulawar su kansu ‘yan sahayoniyar da kuma Amurka.
Majiyar Asibitin “Audah” ta sanar da cewa an kai shahida 4 da kuma wadanda su ka jikkata sanadiyyar hare-haren na sojojin mamaya a wurin raba kayan agaji dake kan titin “Salahuddin” a tsakiyar zirin Gaza.
A arewacin yankin Gaza kuwa wasu samarin Falasdinawa 4 sun yi shahada bayan da jiragen yakin HKI su ka kai hari a kusa da makarantar “Usamatu Bin Zayd” dake yankin Safdhawi.
Wasu jiragen yakin na ‘yan mamaya sun kai wasu hare-haren a unguwar “Basrah’ dake birnin Gaza. Ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko yin shahada.
A kusa da mashigar ‘al-Buraij’ ma sojojin mamayar sun kai hari da jirgin sama maras matuki akan mutane da suka yi cirko-cirko suna tsumayen kayan agaji.
Wasu wuraren da aka sami shahidai sun hada da sansanin ‘yan hijira na “Nusairat’ da “Muwasi” a Khan-Yunus, sai kuma “Badhnus-samin”.
Tun a makwannin da su ka gabata ne dai MDD ta sanar da cewa ba za ta shiga cikin tsarin dake karkashin HKI da Amurka ba, na raba kayan agaji, saboda manufarsa korar Falasdinawa daga gidajensu. Ita kuwa kungiyar Hamas ta ce, wuraren na rabon agaji sun zama tarko kisa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sami Nasara Akan Korea Ta Arewa Akarkashin Share Fagen Shiga Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon
Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta sami nasarar akan abokiyar karawarta ta kasar Korea Ta Arewa da kwallaye uku masu kyau a wasan da aka yi a filin wasa na “Azadi” na Tehran.
Kasashen biyu dai suna a karkashin; bangare na uku a Asiya saboda share fagen kai wa ga shiga gasar cin kofin kwallon duniya na 2026.
Dan wasa mai suna Muhammad Muhibbi ne ya ci kwallon farko, a mintuna 74 da fara wasan, sai kuma Mahdi Darimi a mintuna 77, sa Amir Husain Husain zadeh, a minti 3 da aka kara, bayan cikar mituna 90.
A bangaren kungiyar kwallon kafa ta Korea Ta Arewa kuwa, ta kammala wasannin nata da ‘yan wasa 10 bayan da aka kori daya daga cikinsu saboda adaidai mintuna na 66 daga fara wasa.
Sauran kungiyoyin da suke cikin wannan bangare na uku, da kuma su ka yi wasa a wannan rana, sun hada Uzbakistan da ta ci Qatar 3-0 a birnin Tashqand. Ita kuwa Kyrkizistan ta yi daya da daya da Hadaddiyar Daular Larabawa.
Iran ce a gaba a cikin bangaren nasu na uku; da take da maki 23, sai kuma Uzbakistan mai binta da maki 21, ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa tana da maki 15, yayin da Qatar take da maki 13. Kasar Kyrkizitan tana da maki 8, sai kuma Korea Ta Arewa mai maki 3.