HausaTv:
2025-07-28@00:29:30 GMT

Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji

Published: 11th, June 2025 GMT

Sojojin HKI sun kai hari akan Falasdinawan da su ka yi cincirindo domin karbar abinci da hakan ya yi sanadiyyar shahadar da dama daga cikinsu.

Tun da safiyar yau Laraba ne dai sojojin HKI su ka rika kai hare-hare akan cibiyoyin cibiyoyin raba agaji wadanda dama suna a karkashin kulawar su kansu ‘yan sahayoniyar da kuma Amurka.

Har ila yau hare-haren sun shafi gidajen fararen hula a cikin wasu unguwanni na zirin Gaza.

Majiyar Asibitin “Audah” ta sanar da cewa an kai shahida 4 da kuma wadanda su ka jikkata sanadiyyar hare-haren na sojojin mamaya a wurin raba kayan agaji dake kan titin “Salahuddin” a tsakiyar zirin Gaza.

A arewacin yankin Gaza kuwa wasu samarin Falasdinawa 4 sun yi shahada bayan da jiragen yakin HKI su ka kai hari a kusa da makarantar “Usamatu Bin Zayd” dake yankin Safdhawi.

Wasu jiragen yakin na ‘yan mamaya sun kai wasu hare-haren a unguwar “Basrah’ dake birnin Gaza. Ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko yin shahada.

A kusa da mashigar ‘al-Buraij’ ma sojojin mamayar sun kai hari da jirgin sama maras matuki akan mutane da suka yi cirko-cirko suna tsumayen kayan agaji.

Wasu wuraren da aka sami shahidai sun hada da sansanin ‘yan hijira na “Nusairat’ da “Muwasi” a Khan-Yunus, sai kuma  “Badhnus-samin”.

Tun a makwannin da su ka gabata ne dai MDD ta sanar da cewa ba za ta shiga cikin tsarin dake karkashin HKI da Amurka ba, na raba kayan agaji, saboda manufarsa korar Falasdinawa daga gidajensu. Ita kuwa kungiyar Hamas ta ce, wuraren na rabon agaji sun zama tarko kisa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?

Shugaban kasar Iran ya yi kiran cewa: Ina masu fafutukar kare hakkin bil’adama suke a bala’in Gaza?

Shugaban kasar Iran Dr. Masoud Pezeshkian ya jaddada muhimmancin sauya salon tafiyar da gwamnati da kuma karfafa alaka da kasashen da ke makwabtaka da ita, yana mai cewa masu takama da kare hakkin bil’adama suna nuna fuska biyu a aikinsu, inda suka yi shiru kan munanan laifukan da ake yi wa al’ummar Gaza.

A safiyar yau ne shugaba Pezeshkian ya isa ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda ya gana da mataimakan ministoci da daraktocin ma’aikatar.

A lokacin da yake jawabi a taron, shugaban ya ce, “Tun da yake dan majalisar shawarar Musulunci bai canza ba, har yanzu shi mutum daya ne, dole ne al’umma su kasance masu jajircewa da kwarewa tare da ci gaba da yin aiki tukuru, sun mika ragamar mulki ga ministoci da gwamnonin larduna, wasu kura-kurai dole ne a gyara su, me yasa gwamna ba zai iya yin abin da shi yake yi ba?”

Pezeshkian ya kara da cewa, “Idan aka bi tsarin manufofin – wato manyan tsare-tsare, kuma aka ba da iko ga wadanda ke cikin wannan fanni, aikin zai ci gaba. Idan kuskure ya faru, dole ne a gyara shi. Daga nan ne yanayin kasar zai inganta.” Dole ne kuma gwamnoni su mika mulki ga shugabannin kananan hukumomi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta ce Ta Tsaida Yaki A Gaza Na Wani Lokaci
  • Sojojin HKI Sun Kutsa cikin Jirgin Ruwan “Hanzala” Dake Son Karya Killace Yankin Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
  • Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
  • Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza