HausaTv:
2025-06-12@22:06:40 GMT

 Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi

Published: 11th, June 2025 GMT

Shugaban kasar ta Amurka wanda ya gabatar da jawabi a gaban sojojin kasar a sansanin ‘Fort Bragg’ dake Jahar North Carolina ya  bayyana cewa; Jahar Los Angeles tana fuskantar mamaya daga makiya ‘yan kasashen waje.”

Har ila yau shugaban na Amurka ya ce; Ba za mu bari a rika kai wa jami’an tsaron gwamnatin tarayya hari ba, ba kuma za mu bari a mamaye wani gari daga cikin garuruwan Amurka ba.

Shugaban kasar ta Amurka ya kuma ce; Abinda birnin  Los Angeles yake fuskanta hari ne daga kowace kusurwa da ‘yan daba suke yi, kuma suna dauke da tutocin kasashen waje.”

Birnin Los Angeles yana fuskantar gangami da Zanga-zanga saboda nuna kin amincewa da Shirin korar ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba.

 An sami sabani da rashin jituwa a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma ta jaha akan matakin da ya kamata a dauka domin magance matsalar bakin hauren.

Gwamnan Jahar ta Califonia ya zargi shugaban kasar Donald Tump da kama-karya saboda aikewa da sojoji akan titunan birnin domin fuskantar masu gangamin da Zanga-zangar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci

Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci da ke kawo karshen zaman tankiyar da aka soma tsakanin kasashen biyu tun bayan hawan Donald Trump karagar mulki.

Kasashen biyu sun cimma matsaya a kan kan cinikin wani rukini na ma’adinai da Chinar ke fitarwa, wadanda ake kira da sunan Terres Rares, wadanda ake yi amfani da shi wajen samar da lantarki da kuma makamashin da ake sabbintawa.

An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m

A baya a taron kasar Switzerland, Washington ta amince da rage haraji kan kayayyakin kasar China daga kashi 145 zuwa kashi 30 cikin 100, don musanya makamancin wannan mataki da Beijing ta dauka daga kashi 125% zuwa 10% kan kayayyakin Amurka, na tsawon kwanaki 90.

Shugaban Gwamnatin Jamus, Frederich Merz, ya yi marhabin da yarjejeniyar kasuwanci da aka cimma tsakanin Washington da Beijing a birnin Landan na Birtaniya.

Merz ya ce yana maraba da wannan yarjejeniya, kuma yana matukar Kungiyar Tarayyar Turai za ta yi nasara wajen rage rikice-rikicen kasuwanci da Amurka.

A watan Mayun da ya gabata ne China da Amurka suka cimma yarjejeniyar jinkirta aiwatar da sabon tsarin biyan harajin da suka lafta wa juna har sai bayan kwanaki 90, matakin da tun a lokacin aka yi tsammanin zai iya kawo karshen zaman tankiyar da ake yi tsakanin kasashen biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.

Sai dai a farkon makon nan ne China ta tabbatar da cewa wakilanta za su gana da takwarorinsu na Amurka a kasar Birtaniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka
  • Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro
  • Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya
  • Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata