Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza
Published: 10th, June 2025 GMT
Al’ummu daga dukkan sassan duniya suna mayar da martaninsu cikin fushi bayan sace jirgin ruwa Madeleine mai dauke kayayyakin jin kai zuwa Gaza
Kwamandojin sojojin mamayar Isra’ila sun yi garkuwa da jirgin ruwan farare hula Madeleine, wanda ke yunkurin karya killace yankin Zirin Gaza da aka yi a kokarinsu na shigar da kayan agaji ga al’ummar yankin da suka rage.
A wani sabon laifin da ya saba wa dukkanin ka’idojin kasa da kasa da na jin kai, sojojin mamayar Isra’ila sun yi awon gaba da jirgin ruwan da kekokarin karya killace Gaza na Madeleine, tare da yin awungaba da masu fafutuka na kasa da kasa da ke cikin jirgin. Jirgin yana kan hanyar zuwa zirin Gaza dauke da kayan agaji ne.
Sojojin mamaya sun kai jirgin zuwa tashar jiragen ruwa ta Ashdod domin yi wa masu fafutuka tambayoyi tare da tabbatar da ko su wane ne su, har zuwa lokacin da ake yi musu tambayoyi a wani sansanin sojin ruwa da ke tashar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IMF na Shirin aikewa da wata tawaga zuwa Senegal domin tattauna batun basussukan kaaar
Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya fada a wannan alhamis cewa yana shirin aikewa da tawaga zuwa kasar Senegal a cikin watan Augusta domin tattauna yadda aza magance matsalar basussukan da ke kan kasar da kuma fara tattaunawa kan tsarin sabon shirin lamuni.
Kasar Senegal na fama da bashin biliyoyin daloli da gwamnatin da ta shude ta karba, lamarin da ya sanya asusun lamuni na duniya IMF ya dakatar da shirin ba da lamuni ga kasar.
A nasa bangaren kuma, wani mai magana da yawun IMF ya ce, “Asusun na bukatar karin bayanai kafin ya karfafa kimanta halin da ake ciki na basussukan kasar Senegal, sannan yana bukatar yarjejeniya kan muhimman matakan gyara.”
Ya kara da cewa, “Da zarar mun cimma matsaya kan manyan matakan gyara, hukumar ta IMF za ta sake yin nazari kan batun, yana mai bayyana cewa “zai yiwu a cimma matsaya kan wadannan matakan nan da makonni masu zuwa.”
Kakakin ya kara da cewa “Hukumar lamuni ta duniya IMF ta yi kiyasi bisa ga sabbin bayanai daga hukumomin kasar Senegal cewa basusukan da aka boye wanda gwamnatin da ta gabata ta karb, sun kai dala biliyan 11.3 a karshen shekarar 2023. Wannan ya hada da wani kaso na bashin kamfanonin gwamnati da aka kiyasta kusan kashi 7.4% na GDP.”
Kakakin IMF ya ce zai ba da bayanai ga hukumar kan yadda lamarin ya faru , yana mai cewa “IMF na gudanar da bincike na cikin gida da tantancewa a matsayin wani bangare na rashin bayar da rahotonni da suka dace.”