Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza
Published: 10th, June 2025 GMT
Al’ummu daga dukkan sassan duniya suna mayar da martaninsu cikin fushi bayan sace jirgin ruwa Madeleine mai dauke kayayyakin jin kai zuwa Gaza
Kwamandojin sojojin mamayar Isra’ila sun yi garkuwa da jirgin ruwan farare hula Madeleine, wanda ke yunkurin karya killace yankin Zirin Gaza da aka yi a kokarinsu na shigar da kayan agaji ga al’ummar yankin da suka rage.
A wani sabon laifin da ya saba wa dukkanin ka’idojin kasa da kasa da na jin kai, sojojin mamayar Isra’ila sun yi awon gaba da jirgin ruwan da kekokarin karya killace Gaza na Madeleine, tare da yin awungaba da masu fafutuka na kasa da kasa da ke cikin jirgin. Jirgin yana kan hanyar zuwa zirin Gaza dauke da kayan agaji ne.
Sojojin mamaya sun kai jirgin zuwa tashar jiragen ruwa ta Ashdod domin yi wa masu fafutuka tambayoyi tare da tabbatar da ko su wane ne su, har zuwa lokacin da ake yi musu tambayoyi a wani sansanin sojin ruwa da ke tashar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa
Kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, ta kira taro karo na 63 mai taken “Ba da tallafin ciniki” a jiya Talata a birnin Geneva. Yayin da aka tattauna bisa ajandar “Makomar hadin gwiwar kasashe masu tasowa da saurin bunkasuwa”, Sin ta yi cikakken bayani kan dabaru, da fasahohi da Sin take da su a fannin tallafawa sauran kasashe masu tasowa wajen gina manyan ababen more rayuwa, da gaggauta karfin samar da tsare-tsaren cinikayya, matakin da ya samu karbuwa matuka daga mahalarta taron.
A bangaren nahiyar Afirka, kasar Mozamqiue ta darajanta kokarin da Sin take yi na karawa kasashe masu tasowa kwarin gwiwar gina ingantattun manyan ababen more rayuwa, da gaggauta karfin samar da tsare-tsare, karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa, matakin ya bayyana niyyar Sin na cika alkawuran da take yi na tabbatar da tsarin gudanar da cinikayya tsakanin mabambantan bangarori, da amfanar da al’ummun kasashensu. A bangaren wakilcin kasashe mafiya karancin ci gaba, wakilin Nepal ya bayyana godiya ga taimakon da Sin take ba su, a bangaren zamanantar da na’urorin kwastam, da kafa dokar ciniki, da samun ci gaba mai dogaro da yanar gizo da sauransu.
Ban da wannan kuma, tawagar Kamaru ta yi godiya ga gudunmawar da Sin take bayarwa ga nahiyar Afirka a bangaren gina manyan ababen more rayuwa, da tabbatar da zaman doka da oda da habaka karfinsu, matakan da suka ingiza bunkasar nahiyar a dukkanin fannoni masu dorewa. A nata bangare, tawagar kasar Tanzaniya, ta jinjinawa tallafin da Sin take baiwa kasashen Afirka a bangaren ciniki, tana godiya da kokarin da Sin take yi na zurfafa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, bisa hanyar kirkire-kikire da take bullowa da su, ta yadda kasashe masu tasowa za su shiga a dama da su cikin tsarin cinikin duniya yadda ya kamata. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp