Aminiya:
2025-06-13@10:03:16 GMT

Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza

Published: 9th, June 2025 GMT

Sojojin Isra’ila sun ƙwace wani jirgi da ke ɗauke da kayan tallafi mai suna Madleen wanda ke kan hanyara a zuwa Gaza, sannan suka karkata akalar shi zuwa Isra’ila.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ilan ta fitar da tsakar daren Lahadi ta bayyana cewa za a mayar da masu fafutukar da ke cikin jirgin zuwa ƙasashensu.

Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba Zaɓen 2027 ba — ACF

Sanarwa da aka wallafa a X, ma’aikatar ta ce jirgin yana “kan hanyarsa zuwa gaɓar tekun Isra’ila” kuma “ana sa ran fasinjojin za su koma ƙasashensu.”

Ƙungiyar Freedom Flotilla Coalition ta ce sojojin Isra’ila sun “yi garkuwa” da masu fafutukar da ke cikin jirgin na Madleen, ciki har da Greta Thunberg, ’yar kasar Sweden da ke hankoron kare muhalli.

Tun da farko, sojojin ruwan Isra’ila sun shiga jirgin na Madleen a cikin tekun ƙasa da ƙasa, a cewar ƙungiyar, wadda ta kuma ce an katse sadarwa da jirgin.

Hotunan kai tsaye da aka nuna a baya sun nuna jiragen ruwa na Isra’ila sun kewaye jirgin, inda sojoji suke umartar masu fafutukar da ke cikin jirgin su ɗaga hannayensu sama.

‘Yar Majalisar Tarayyar Faransa ‘yar asalin Falasɗinu, Rima Hassan, ta ce an kunna ƙararrawa a cikin jirgin na Madleen bayan da jiragen sama marasa matuƙa suka fesa wani farin ruwa a jirgin.

Babbar Jami’a ta Musamman ta Majalisar Dinkin Duniya, Francesca Albanese, ta tabbatar da cewa an ga jiragen sama marasa matuƙa guda biyu a sama, tana bayyana su da cewa “waɗanda ke da hatsari.”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ila ta ce sojojin ruwa sun umarci jirgin Madleen da ya sauya hanya saboda kusancinsa da abin da suka kira “yankin da ba a shiga.”

Jirgin Madleen, wanda yake da tsawon mita 18, ya fara tafiya zuwa Gaza a ranar 1 ga watan Yuni daga tashar jirgin ruwa ta San Giovanni Li Cuti a Catania, Sicily, a matsayin wani ɓangare na sabon shirin da ƙungiyar Freedom Flotilla Coalition ta shirya don karya takunkumin Isra’ila da isar da tallafi zuwa Gaza.

Jimillar mutane 12 ne ke cikin jirgin, ciki har da masu fafutuka 11 da kuma ɗan jarida guda ɗaya.

A cewar masu shirya tafiyar, jirgin yana ɗauke da kayayyakin tallafi masu matukar muhimmanci ga mutanen Gaza, ciki har da madarar jarirai, da fulawa, da shinkafa, da maganin jarirai, da kayayyakin tsafta na mata, da kayan tace ruwa, da magunguna , sandunan guragu, da kuma kayan taimakon yara masu nakasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka ba tare da taɓarɓarewa nan da shekaru uku masu zuwa.

Bankin ya yi hasashen haɓakar ma’aunin tattalin arzikin cikin gida, GDP da kashi 3.6 cikin 100 a shekarar 2025, sai kashi 3.7 a shekarar 2026 da kuma kashi 3.8 a shekarar 2027.

Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci

A cewar sabon rahoton tattalin arzikin duniya da Bankin ya fitar, ana sa ran za a tallafa wa matsakaicin lokaci na Nijeriya ta hanyar samar da ingantattun albarkatun mai, da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi, da kuma farfado da ƙwarin gwiwar masu zuba jari.

Rahoton ya yi nuni da cewa, yayin da tattalin arzikin kasar ke shirin fadada, kalubale irin su hauhawar farashin kayayyaki, da matsalar canjin kudi, da kuma gibin kasafin kudi na ci gaba da zama babbar barazana ga ci gaba mai ɗorewa.

Bankin ya kuma kara da cewa, aiwatar da sauye-sauye a fannin tattalin arziki da gwamnatin Nijeriya ke yi, musamman ta fuskar farashin makamashi da tattara kuɗaɗen shiga, da sarrafa kuɗaɗen musaya, zai taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da waɗannan hasashen ci gaban.

Ana sa ran ci gaban Nijeriya a shekarar 2025 zai kasance matsakaici da kashi 3.3 cikin 100, yayin da matsalolin tsarin ke ci gaba da yin la’akari da saurin farfadowar tattalin arziki.

Bankin Duniya ya yi kira ga masu tsara manufofin Nijeriya da su ba da fifiko ga sauye-sauyen tsarin da ke inganta ci gaban kamfanoni masu zaman kansu, inganta ababen more rayuwa, da inganta jarin ɗan Adam don ɗorewar bunkasar tattalin arziki na dogon lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya
  • Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
  • Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • Gidauniyar Hind Rajab ta kai karar Isra’ila kan harin jirgin ruwan Madleen
  • Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza