Aminiya:
2025-07-25@04:27:54 GMT

Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza

Published: 9th, June 2025 GMT

Sojojin Isra’ila sun ƙwace wani jirgi da ke ɗauke da kayan tallafi mai suna Madleen wanda ke kan hanyara a zuwa Gaza, sannan suka karkata akalar shi zuwa Isra’ila.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ilan ta fitar da tsakar daren Lahadi ta bayyana cewa za a mayar da masu fafutukar da ke cikin jirgin zuwa ƙasashensu.

Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba Zaɓen 2027 ba — ACF

Sanarwa da aka wallafa a X, ma’aikatar ta ce jirgin yana “kan hanyarsa zuwa gaɓar tekun Isra’ila” kuma “ana sa ran fasinjojin za su koma ƙasashensu.”

Ƙungiyar Freedom Flotilla Coalition ta ce sojojin Isra’ila sun “yi garkuwa” da masu fafutukar da ke cikin jirgin na Madleen, ciki har da Greta Thunberg, ’yar kasar Sweden da ke hankoron kare muhalli.

Tun da farko, sojojin ruwan Isra’ila sun shiga jirgin na Madleen a cikin tekun ƙasa da ƙasa, a cewar ƙungiyar, wadda ta kuma ce an katse sadarwa da jirgin.

Hotunan kai tsaye da aka nuna a baya sun nuna jiragen ruwa na Isra’ila sun kewaye jirgin, inda sojoji suke umartar masu fafutukar da ke cikin jirgin su ɗaga hannayensu sama.

‘Yar Majalisar Tarayyar Faransa ‘yar asalin Falasɗinu, Rima Hassan, ta ce an kunna ƙararrawa a cikin jirgin na Madleen bayan da jiragen sama marasa matuƙa suka fesa wani farin ruwa a jirgin.

Babbar Jami’a ta Musamman ta Majalisar Dinkin Duniya, Francesca Albanese, ta tabbatar da cewa an ga jiragen sama marasa matuƙa guda biyu a sama, tana bayyana su da cewa “waɗanda ke da hatsari.”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ila ta ce sojojin ruwa sun umarci jirgin Madleen da ya sauya hanya saboda kusancinsa da abin da suka kira “yankin da ba a shiga.”

Jirgin Madleen, wanda yake da tsawon mita 18, ya fara tafiya zuwa Gaza a ranar 1 ga watan Yuni daga tashar jirgin ruwa ta San Giovanni Li Cuti a Catania, Sicily, a matsayin wani ɓangare na sabon shirin da ƙungiyar Freedom Flotilla Coalition ta shirya don karya takunkumin Isra’ila da isar da tallafi zuwa Gaza.

Jimillar mutane 12 ne ke cikin jirgin, ciki har da masu fafutuka 11 da kuma ɗan jarida guda ɗaya.

A cewar masu shirya tafiyar, jirgin yana ɗauke da kayayyakin tallafi masu matukar muhimmanci ga mutanen Gaza, ciki har da madarar jarirai, da fulawa, da shinkafa, da maganin jarirai, da kayayyakin tsafta na mata, da kayan tace ruwa, da magunguna , sandunan guragu, da kuma kayan taimakon yara masu nakasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe

Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu.

Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru.

Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace

Dr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu.

Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi ta kasa da kasa ACF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin wajen Jamus (GFFO), sun raba kayan agajin ceton rai ga magidanta 566 a kananan hukumomin Fika da Potiskum da lamarin ya shafa.

Kazalika, kididdigar haɗin gwiwa ta hukumar ta SEMA da ACF suka fitar ta ba da fifiko ga iyalan da wadanda wannan iftila’i ya fi shafa kai tsaye musamman waɗanda suka rasa gidajensu, da kayan masarufi, ko damar samun wani taimakon na tsafta.

Mohammed Liman Kingimi, na kungiyar ACF, ya tabbatar da kudurin kungiyar na kara ba da taimako bisa ga yadda bukatun hakan suka taso.

Ya ce kungiyar na kuma shirye-shiryen kaddamar da tallafin abinci ga magidanta 566 don rage musu radadi.

Dokta Goje ya buqaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata sannan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kare al’umma masu rauni ta hanyar xaukar matakan gaggawa.

Ya kuma jaddada qudirin hukumar cewa kullum a shirye take wajen gudanar da ayyukanta kamar yadda ya dace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila