Leadership News Hausa:
2025-06-12@22:57:09 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

Published: 11th, June 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

Wani ganau mai suna Kespan Iliya wanda shi ma mazaunin unguwar ne ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan unguwar na cikin barci lokacin da ‘yan bindigar suka iso cikin shigar kwamandoji, inda suka rika harbe-harbe kan mazauna unguwar.

 

LEADERSHIP ta fahimci cewa, sama da gidaje 96 ne kuma aka kone a Gyenbwas, al’ummar gundumar Langai ta karamar hukumar Mangu a yayin harin.

 

Kokarin jin ta bakin jami’im yada labarai na rundunar ‘Operation Save Haven (OPSH)’, Manjo Samson Zhakom ya ci tura domin wayarsa a kashe take a lokacin rubuta wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu

Mahara sun kone gidaje akalla 96 a yankin Gyenbwas na gundumar Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Mazauna yankin sun kuma yi zargin cewa maharan sun kuma kwashe musu kayan abinci da katifu da kuma shanu da sauran kayayyaki.

Alhaji Yakubu Umar, wanda kuma shi ne Madugun Langai ne ya shaida wa Aminiya hakan a ranar Talata.

A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alau — Gwamnatin Borno Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara

Ya kuma ce bayan mutum biyun da aka kashe musu ranar Litinin, sun kuma kara samo gawar mutum daya a yankin, wanda hakan ya kai adadin mutanen da aka kashe yayin harin zuwa uku.

Mazauna yankin dai na zargin ’yan kabilar Birom da kai musu harin, kodayake su kuma sun musanta hakan.

A cewar Alhaji Yakubu, “Ba a taba yi mana irin wannan ta’addancin ba. maharan sun kone kayan amfani masu yawa ciki har da sutturu da kuma kayan abinci. Sannan sun sace kayayyakinmu na miliyoyin naira. Mu a gaskiya muna zaune da kowa lafiya a nan, shi ya sa ma harin ya yi matukar daure mana kai.

Daga nan sai ya yi kira da gwamnati da ta binciki harin domin ta hukunta wadanda ke da hannu a ciki sannan ta kai wa wadanda suka yi asara tallafi.

Ba mu muka kai harin ba – Birom

Sai dai Kungiyar Matasa Birom (BYM) ta karyata labarin kai harin, inda ta bayyana shi a matsayin na kanzon kurege.

Shugaban kungiyar, Dalyop Solomon, ya ce, “Jiya akwai mambobinmu uku da aka kai wa hari yayin da suke aiki a gonakinsu, wadanda yanzu haka suna asibiti ana kula da su. Abin da muka sani kawai shi ne mutanenmu na cikin fargaba, kawai Fulani na fitowa ne saboda su samu dalilin kai mana hari.

“Amma ya kamata su sani, duk lokacin da suka kai mana hari, muna da ’yancin kare kanmu. Ba mamaki abin da ya faru ke nan. An zo kawo musu hari suka fatattaki maharan har zuwa maboyarsu, amma mu ba mu taba kai wa Fulani wani hari ba,” in ji Dalyop.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya
  • Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu
  • Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
  • Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya
  • Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe