Jiragen ruwan wadanda aka bai  wa sunan: “Jajurcewa” za su tashi ne daga Tunisiya jim kadan bayan da sojojin HKI su ka hana wani jirgin ruwan dake dauke da masu fafutuka daga kasashen turai,isa gabar ruwan Gaza.

Jirgin ruwan na ” Jajurcewa’ zai bi ta ruwan Libiya, sannan Masar daga can kuma ya nufi gabar ruwan Gaza.

Jiragen ruwan dai suna dauke da masu fafutuka 7,000 daga kasashen Tunisiya, Moroko, Aljariya, Murtaniya, da Libiya.

Kwamitin kasa da kasa domin karya killace Gaza, wanda ya shirya wannan tafiyar, ya kuma yi wani kiran ga ‘yan fafutuka a duniya da su shirya wasu tafiye-tafiyen ta ruwa zuwa Gaza, domin kawo karshen killace yankin da aka yi tun 2007.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza

Aƙalla Falasɗinawa 13 ne suka rasu a ranar Asabar a Gaza, sakamakon hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai.

Mutum shida daga cikinsu sun mutu ne a kusa da cibiyar rabon tallafi a garin Rafah da ke Kudancin Gaza.

2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Gaza, Mahmud Bassal, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safe, a kusa da gadar Al-Alam.

Mutane sun taru a wajen domin karɓar tallafi daga wata cibiya da Gidauniyar Gaza Humanitarian Foundation (GHF) ke jagoranta, wadda ke samun goyon bayan Amurka, kimanin kilomita ɗaya daga wajen.

Shaidu sun ce, da zarar wasu suka yi ƙoƙarin matsawa kusa da cibiyar agajin, sai sojojin Isra’ila da ke cikin motocin yaƙi su fara harbi a sama, kafin daga baya suka buɗe wa mutane wuta.

Dakarun Isra’ila sun ce suna bincike kan lamarin.

Wannan ba shi ne karon farko da aka kashe mutane a kusa da cibiyar agaji ta Al-Alam ba.

Gidauniyar GHF ta fara rabon tallafin ne tun ƙarshen watan Mayu, bayan Isra’ila ta sassauta wani takunkumi da ta ɗora wa Gaza na sama da watanni biyu.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta ƙi haɗa kai da GHF saboda rashin tabbas kan adalci, kuma ta yi gargaɗin cewa kusan dukkanin al’ummar Gaza sama da mutum miliyan biyu na fuskantar barazanar yunwa.

A wani ɓangare na Gaza a ranar Asabar, an kuma kashe mutum bakwai sakamakon wani hari da jirgin saman Isra’ila ya kai wani gida kusa da Asibitin Al-Shifa da ke birnin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun ce shi ma za su binciki wannan harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
  • Jirgin Ruwa “Madeleine” Dake Son Karya Takunkumin Gaza Yana Ci Gaba Da Tafiya
  • Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
  • Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
  • Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza
  • 2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe