Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla
Published: 7th, June 2025 GMT
A rana ta biyu tabukuwan babbar salla, sojojin HKI suna ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyasahi da kuma rusa matsugunansu a yankin Gaza.
A yau Asabar kadai gwamman Falasdinawa ne su ka yi shahada a cikin sansanonin da Falasdinawa suke gudun hijira a cikinsu.
An sami shahidai 5 da kuma wasu mutane biyu da su ka jikkata a kusa da cibiyar rana kayan agaji a yammacin Rafah dake kudancin zirin Gaza.
A yammacin birnin Khan-Yunus kuwa wasu Faladinawa 12 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 40 su ka jikkata saboda harin da ‘yan sayahoniyar su ka kai wa sansaninsu.
A arewacin Khan-Yunus kuwa, sojojin mamayar sun ruguza gidajen Falasdinawa da dama.
A kusa da cibiyar kiwon lafiya ta ” Majma’u -Shifa” dake yammacin birnin Gaza, adadin shahidai ya kai 7 wasu biyu kuwa su ka jikkata.
Daga lokacin da HKI ta shelanta yaki akan mutanen Gaza a 2023, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 54,677, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 125,530.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Shugaba Xi ya kara da cewa, a halin da ake ciki yanzu, duniya na fuskantar sauye-sauye irin wadanda ba a taba gani ba kuma cikin sauri. Don haka, kamata ya yi kasashen biyu masu dadaddun wayewar kai su zurfafa koyi da juna, da shigar da sabon kuzari cikin gina cikakken salon hadin kai, bisa manyan tsare-tsare tsakaninsu, kana su tattaro karfin wayewar kai don gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.
A wani ci gaban kuma, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping wato ministan raya al’adu da yawon bude ido na kasar Sun Yeli, ya halarci bikin bude babban gidan adana kayan tarihin na GEM bisa gayyatar gwamnatin Masar. Kafin bikin, shugaba al-Sisi ya gana tare da gudanar da gajeriyar tattaunawa da Sun Yeli. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA