A rana ta biyu tabukuwan  babbar salla, sojojin HKI suna ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyasahi da kuma rusa matsugunansu a yankin Gaza.

A yau Asabar kadai gwamman Falasdinawa ne su ka yi shahada a cikin sansanonin da Falasdinawa suke gudun hijira a cikinsu.

An sami shahidai 5  da kuma wasu mutane  biyu da su ka jikkata a kusa da cibiyar rana kayan agaji a yammacin Rafah dake kudancin zirin Gaza.

A yammacin birnin Khan-Yunus kuwa wasu Faladinawa 12 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 40 su ka jikkata saboda harin da ‘yan sayahoniyar su ka kai wa sansaninsu.

A arewacin Khan-Yunus kuwa, sojojin mamayar sun ruguza gidajen Falasdinawa da dama.

A kusa da cibiyar kiwon lafiya ta ” Majma’u -Shifa” dake yammacin birnin Gaza, adadin shahidai ya kai 7 wasu biyu kuwa su ka jikkata.

Daga lokacin da HKI ta shelanta yaki akan mutanen Gaza a 2023, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 54,677, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 125,530.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
  • An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai