Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Sake kunna ‘hanyar tayar da hankali’ zai gamu da martani mai ƙarfi na Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Fitar da kudiri kan Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta yi ba zai shafi kudurin al’ummar Iran ba ko kuma ci gaban shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya.

A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Iran a yammacin ranar Talata, Baqa’i ya yi la’akari da dukkanin rahotanni da kudurorin da suka shafi siyasa. Ya kuma kara da cewa Iran ba ta keta hurumin da ya rataya a wuyanta ba, kuma kasashen yammacin turai suna dora barazanarsu ne kan zargin da aka shafe shekaru 20 ana yi. Ya jaddada cewa Iran ba za ta yi watsi da hakkinta na inganta sinadarin Uranium ba.

Ya yi nuni da cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, Rafa’el Grossi, yana aiki ne da son zuciya, da kuma maimaita labaran bangarorin da ke adawa da Iran, ya kara da cewa, mayar da “hanyar tayar da hankali” za ta fuskanci martani mai karfi na Iran.

Dangane da matsayin Sanya batun Iran a gaba a hukumar ta IAEA da kuma barazanar da kasashen Turai ke yi na fitar da wani kuduri a taron majalisar alkalan hukumar IAEA da ke gudana a halin yanzu, ya bayyana cewa, batun nukiliyar Iran wani kuduri ne na siyasa kawai tun da farko, a lokacin da ya shiga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kuma kafin nan, lokacin da ake kallon lamarin a matsayin wani lamari mai yaduwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa

Iran ta yi Allah-wadai da wani kuduri da ta danganta da na siyasa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta dauka, tana mai cewa ba shi da tushe na fasaha ko doka.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) da ma’aikatar harkokin wajen kasar sun fitar da sanarwar hadin gwiwa yau Alhamis bayan da majalisar gwamnonin hukumar ta IAEA suka amince da wani kuduri da ke zargin Iran da rashin cika alkawuran da ta dauka na nukiliya.

Kuri’u 19 ne suka amince da kudurin wanda Amurka da Birtaniya da Faransa da Jamus suka tsara.

Kasashen Rasha, China da Burkina Faso sun kada kuri’ar kin amincewa da shi, Yayin da kasashen Afirka ta Kudu, Indiya, Pakistan, Masar, Indonesia da Brazil suka ce su kam ba ruwan su.

Sanarwar da Iran ta fitar dangane da wannan kudiri ta ce, Jamhuriyar Musulunci ba ta da wani zabi face mayar da martani ga wannan kudiri na siyasa.”

Sanarwar ta ce, Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI), Mohammad Eslami, ya ba da umarnin gina sabuwar cibiyar tace uranium a wani wuri mai aminci.

Sabuwar cibiyar za ta kunshi sabbin na’urorin tace uranium na zamani inji sanarwar.

A cikin sanarwar, Tehran ta yi tir da kudirin na “siyasa da son zuciya” na IAEA  Wanda Amurka da manyan kasashen Turai uku – Faransa, Jamus da Birtaniya suka tsara.

Iran ta kuma yi tir da shirun da Amurka da kawayenta na Turai suka yi wajen tinkarar yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kin mutunta yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka tabbatar da sake ganawa a karo na shida a ranar Lahadi mai zuwa game da shirin nukiliyar Iran wanda a’a gudanar a birnin Muscat a shiga stakanin kasar Oman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Iran Ta Ce: Rashin Dakatar Da Uranium Da Dage Takunkumi Sune Hanyar Warware Takaddamar Da Ita
  • Iran: Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Tace Zata Maida Martani Kan Hukumar IAEA
  • Iran Ta Fara Fidda Takardun Sirri Tsakanin HKI Da Hukumar IAEA
  • WHO : har yanzu kyandar biri na da matukar hadari ga duniya
  • Jami’in Makamashin Nukiyar Iran Ya Ce; Zarge-Zargen Da Ake Yi Kan Shirin Makmashin Nukiliyar Iran Siyasa Ce Kawai
  • Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Babban Darektan Hukumar IAEA Saboda Yadda Yake Mika Wuya Ga Bakar Siyasa