Leadership News Hausa:
2025-07-24@23:30:26 GMT

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

Published: 9th, June 2025 GMT

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

Mutane tara ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a kauyen Kyaramma da ke karamar hukumar Ringim a jihar JIgawa. A cewar rundunar ‘yansandan jihar Jigawa, hatsarin wanda ya afku a ranar Asabar da ta gabata da misalin karfe 2 na rana, ya rutsa da wasu motoci kirar Golf 3 saloon guda biyu tare da jikkata wasu da dama.

Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar  Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan” A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Shiisu Adam ya fitar, ya bayyana cewa daya daga cikin motocin mai lamba Kaduna MKA 687 AY, wani mutum mai shekaru 35 dan karamar hukumar Hadejia, Adamu Sunusi ne ke tuka motar zuwa garin Gujungu daga Abuja. A binciken farko da aka gudanar, Adam ya ce, motocin sun yi taho-mu-gamu ne bayan da motar ta kwace wa dayan direban, lamarin da ya sa dukkanin motocin biyu suka kauce hanya. An dauki matakin gaggawa, inda aka garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Ringim domin kula da lafiyarsu. Kwamishinan ‘yansanda, CP A.T. Abdullahi, ya jajantawa iyalan wadanda suka mutu tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa. Ya kuma bukaci direbobi da su rika bin ka’idojin hanya, su guji wuce gona da iri, sannan su tabbatar da cewa, motocin nasu suna cikakkiyar lafiyar zirga-zirga don gujewa afkuwar hadurra. Sanarwar ta ce, “A yanzu haka fasinjoji 11 suna karbar magani a asibiti kuma suna samun sauki, ana kokarin gano duk wadanda suka rasu domin tuntubar iyalansu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin falasdinawan da su ka yi shahada saboda yunwa sun kai 10.

 Daga lokacin da HKI ta fara amfani da yunwa a matsayin makamin yaki,adadin falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 111.

Wannan adadin yana nuni da yadda rashin abinci ya tsananta a cikin yankin na Gaza saboda yadda Isra’ila ta killace yankin ta hana a shigar da abinci a ciki.

A gefe daya, HKI tana ci gaba da kashe Falasdinawa ta hanyar yi musu kisan kiyashi, da a yau kadai fiye da mutane 80 ne su ka yi shahada. Mafi yawancin wadanda su ka yi shahada a cikin sa’oin nan na baya suna a unguwannin Tallul-Hawa, da Deir-Balah. Haka nan kuma ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a sansanin ‘yan hijira dake Mukhayyam-Shadhi.

 Kungiyoyin kasa da kasa suna ta ci gaba da yin kira da a bude iyakokin Gaza domin a shigar da kayan abinci, sai dai babu faruwar hakan.

A cikin zirin Gaza dai, mutane suna faduwa suna  somewa, wani lokaci mutuwa saboda yunwa, ba kuma babba babu yaro.

Mafi yawancin mutanen da suke mutuwa dai kananan yara ne, jarirai da matasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: Mutane Da Dama Sun Mutu Da Kuma Jikkata Sanadiyyar Gobara A Rumbun Ajiyar Makamai
  •  An Jikkata  Sojojin Sahayoniya 9 Ta Hanyar Take Su Da Mota
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu
  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano