Leadership News Hausa:
2025-06-09@14:11:41 GMT

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

Published: 9th, June 2025 GMT

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

Mutane tara ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a kauyen Kyaramma da ke karamar hukumar Ringim a jihar JIgawa. A cewar rundunar ‘yansandan jihar Jigawa, hatsarin wanda ya afku a ranar Asabar da ta gabata da misalin karfe 2 na rana, ya rutsa da wasu motoci kirar Golf 3 saloon guda biyu tare da jikkata wasu da dama.

Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar  Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan” A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Shiisu Adam ya fitar, ya bayyana cewa daya daga cikin motocin mai lamba Kaduna MKA 687 AY, wani mutum mai shekaru 35 dan karamar hukumar Hadejia, Adamu Sunusi ne ke tuka motar zuwa garin Gujungu daga Abuja. A binciken farko da aka gudanar, Adam ya ce, motocin sun yi taho-mu-gamu ne bayan da motar ta kwace wa dayan direban, lamarin da ya sa dukkanin motocin biyu suka kauce hanya. An dauki matakin gaggawa, inda aka garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Ringim domin kula da lafiyarsu. Kwamishinan ‘yansanda, CP A.T. Abdullahi, ya jajantawa iyalan wadanda suka mutu tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa. Ya kuma bukaci direbobi da su rika bin ka’idojin hanya, su guji wuce gona da iri, sannan su tabbatar da cewa, motocin nasu suna cikakkiyar lafiyar zirga-zirga don gujewa afkuwar hadurra. Sanarwar ta ce, “A yanzu haka fasinjoji 11 suna karbar magani a asibiti kuma suna samun sauki, ana kokarin gano duk wadanda suka rasu domin tuntubar iyalansu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayanan Tsaron HKI

Ministan leken asiri na kasar Iran ya ce asiran tsaron HKI da suka shiga hannun ma’aikatansa sun shafi makaman nukliya na HKI kuma sun nuna kwarewar da jami’an leken asirin kasar suke da shi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan bayanan zasu taimakawa sojojin JMI wajen sanin wuraren da zasu kai hare hare a duk lokacinda yake ya barke tsakanin Iran da haramtacciyar kasar, na makamai da kuma na yanar gizo.

Labarin ya kara da cewa  da jami’an ma’aikatar hukumar leken asiri suka yi kama daga daukar ma’aikatan da suka dace da yin hakan da dabar barun da suke yi amfani da su don kaiwa da bayan da suke bukata ya nuna irin koreawarsu a wannan aikin.

Sannan daga cikin muhimman bayanan da suka samu sun hada da na makaman nukliyar haramtacciyar kasar da kuma dangantakanta da Amurka da kuma kasashen turai rawar da wadan nan kasashe suka taka a karfafa HKI kan makamanta na kissan kaere dangi.

Ministan ya kammala da cewa bayanan da muka samu suna da muhimmanci haka ma hanyar da muka bi muka kai ga bayanan suna da muhimmanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayanan Tsaron HKI
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
  • Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla
  • Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato
  • Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
  • Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane