Wani Lauya Okere Kingdom Nnamdi, wanda ya gabatar da takardu don samun rajistar Jam’iyyar Mutanen Kasa (PPP) a ranar 28 ga Maris, 2025, ya ce bayan wata daya sai INEC ta bayyana cewa ba ta bude adireshin fara yin rajistar sabbin jam’iyyun siyasa.

Jami’an INEC da suka yi magana kan lamarin, sun musanta zarge-zargen.

Sun bayyana cewa duk da cewa an karbi bukatar yin rajista har guda 104, ana ci gaba da gudanar da bincike, sannan kuma tsarin zai fara gudana nan ba da dadewa ba ta hanyar sadarwaar zamani don inganta gaskiya da ingancin aiki.

“Hukumar ta amsa wa masu nema. Ba daidai ba ne a zargi INEC da jinkirin amsa bukatun yin sabbin rajistar. Za a bude Shafin intanet dazarar an kammala duk wani aikace-aikacen da suka cika ka’ida,” in ji wani babban jami’in hukuman.

Mai magana da yawun INEC, Rotimi Oyekanmi, ya sake jaddada cewa kungiyoyin siyasa dole ne su bi doka da oda na tsarin mulkin kasa kafin a yi musu rajista.

“Dole ne INEC ta tabbatar da cewa an bin doka. An bayyana ka’idojin, kuma har idan mai nema bai cika su ba, to ba za a iya masa rajistar ba har sai ya cika,” in ji shi.

Wani mai sharhi kan harkokin shari’a ya bayyana cewa jinkirin aiwatar da rajistar na iya kawo cikas ga shirin zabe, musamman ganin cewa ana sa ran fara zaben fid da gwani na jam’iyya a tsakiyar 2026.

Tsohon shugaban kungiyar siyasa ta kasa da kasa, Farfesa Adele Jinadu ya ce, “Idan masu nema sun bi ka’idojin kundin tsarin mulki da na zabe, babu wata kuntatawa ga rajistar jam’iyya a karkashin tsarin jam’iyyu masu yawa.”

Dakta Dauda Garuba na cibiyar ci gaban dimokiradiyya (CDD) ya kara da cewa, “Idan aka bai wa jam’iyyu damar gudanar da aikinsu cikin ‘yanci da zaman kansu, da yawa daga cikin kalubalen da muke fuskanta a yau ba za su taso ba.”

A ranar 6 ga Maris 2025 ne, majalisar wakilai ta amince da karatu na biyu kan kudirin dokar da ke neman canza rajistar da tsarin kula da jam’iyyun siyasa daga INEC zuwa wani sabon hukuma mai zaman kanta.

Kudirin hadin gwiwa tsakanin shugaban majalisan, Abbas Tajudeen da dan majalisa, Marcus Onobun, wannan kudurin na bayar da shawarar kafa kotun kula da takaddama tsakanin jam’iyyu don warware rikici cikin gida da rikice-rikicen tsakanin jam’iyyun.

An tura kudirin zuwa kwamitocin da ke kula da al’amuran zabe da kuma jam’iyyun siyasa don kara dubawa.

Duk da karuwar kiraye-kiraye na shiga harkokin siyasa, masu nazari da yawa na ganin cewa lokaci na kurewa ga sabbin jam’iyyun wajrn yi musu rajista yadda ya kamata da kuma shirya su kafin zaben 2027.

Shugaban jam’iyyar AA, Barrister Kenneth Udeze ya yi gargadin cewa, “Bai kamata a yi rajistar kowace jam’iyya ba kasa da watanni 12 kafin zabe. Bisa fatan gudanar da zaben fid da gwani na jam’iyyun a tsakiyar 2026, lokaci na kara kuantowa.

A halin yanzu, Nijeriya na da jam’iyyun siyasa 19 da aka tabbatar da rajistarsu, daga cikin 91 bayan INEC ta cire rajistar jam’iyya 74 a shekarar 2020 bisa ga rashin kwazonsu. Jam’iyyun da suka rage sun hada da APC, PDP, LP, NNPP, SDP, ADC, da sauransu.

Irin su, jam’iyyar matasa (YP) da jam’iyyar Boot (BP) sun sake samun rajista ta hanyar hukuncin kotu, wanda ya nuna yiwuwar kalubale na shari’a nan gaba idan INEC ta ci gaba da jinkirin rajista.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jam iyyun siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.

Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.

Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.

Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta