Aminiya:
2025-06-13@10:27:35 GMT

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba

Published: 12th, June 2025 GMT

Wata mummunar guguwa ta yi sanadin mutuwar mutum shida sannan ta jikkata wasu 30 a garin Garba-Chede da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

A cewar wani mazaunin yankin wanda guguwar ta lalata wa gida mai suna Abubakar Dodo, an shafe shekaru masu yawa ba su ga irin ta ba a yankin saboda munin barnar da ta yi.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

A cewarsa, ban da gidaje, guguwar ta kuma lalata makarantu da masallatai da coci-coci, sannan kayan abinci na miliyoyin Naira sun salwanta.

Dagacin garin na Garba-Chede, Kaigama Maigandi, ya yi kira ga Gwamnan Jihar, Agbu Kefas, da ya taimaka wa mutanen yankin da iftila’in ya shafa domin su samu su gyara gidaje da wuraren kasuwancinsu.

A wani labarin kuma, wata tawagar wakilai daga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta ziyarci yankin domin jajanta musu da kuma ganin girman barnar domin ganin irin tallafin da za a yi musu.

Ayarin, wanda ke karkashin jagorancin Dr. Balutu Isa Mohammed, ya yi jaje ga mutanen tare da yi musu alkawarin ba su tallafin muhimman abubuwan da suke bukata domin su rage radadi.

Tawagar ta kuma ziyarci Dagacin garin tare da yi masa bayanin musabbabin zuwansu da kuma ayyukan da suke yi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garba Chede Guguwa Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi

Tsohon Ministan Sufuri kuma jigo a jam’iyyar APC mai mulki, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa ya shirya yin haɗaka da wasu ’yan siyasa domin ƙalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027.

A wata hira da ya yi da BBC, Amaechi ya ce matsin tattalin arziƙi da tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar ne babban dalilin da ya sa ake buƙatar sabuwar haɗaka a siyasa.

Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3 Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu

Ko da yake bai tabbatar da cewa zai tsaya takarar shugaban ƙasa ba, sai dai ya ce komai zai bayyana nan da wani lokaci.

“Lokaci ne kawai zai nuna,” in ji shi.

Wannan bayani na zuws ne ƙasa da wata guda bayan shugabannin APC sun ayyana Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa ɗaya tilo na jam’iyyar a 2027.

Amma Amaechi ya ce har yanzu yana kishin jam’iyyar APC, amma hakan ba yana nufin ya amince da duk abin da gwamnati ke yi ba.

“Idan gwamnati na gazawa wajen ciyar da ƙasa gaba, ba wai saboda kana cikin jam’iyyar sai ka yarda da komai ba. Ka san hakan ba daidai ba ne,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa abu mai kyau shi ne faɗa wa gwamnati gaskiya da kuma bayyana abin da ’yan ƙasa ke buƙata.

Amaechi ya nuna damuwarsa kan yadda yunwa da talauci ke ƙara tsananta a ƙasar, inda ya bayar da misali da wani abin da ya faru da shi.

“Mutane na mutuwa. Mutane na fama da yunwa. Ni kaina na fara jin tasirin yunwar nan,” in ji shi.

“Gaskiya ita ce, ni ma ina jin yunwar nan.”

Ya ce ko da yake mutane na ganin yana da hali, amma matsin tattalin arziƙin yana shafar kowa.

Ya ce bai yanke shawarar tsayawa takara ba tukuna, amma yana ganin zai iya kawo sauyi.

“Tabbas, ina ganin zan iya bayar da gudunmawa mai ma’ana,” in ji shi.

Amaechi ya ce yana tattaunawa da wasu ’yan Najeriya da ke ganin ƙasar na tafiya bisa kuskure domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen kawo sauyi.

Ana kuma samu rahotanni cewa fitattun ’yan adawa kamar Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na Labour Party su ma na shirin kafa haɗaka kafin zaɓen 2027.

Hakazalika, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, wanda ya goyi bayan Tinubu a 2023, kwanan nan ya ce ana ƙoƙarin kafa wata haɗaka da za ta iya ƙalubalantar Shugaba Tinubu.

Sai dai a ’yan watannin nan, wasu ’yan siyasa daga jam’iyyun adawa sun koma APC, abin da ke tayar da hankali cewa Najeriya na iya koma wa tsarin jam’iyya ɗaya.

Amaechi ya ce ƙasar ta tsaya cak, kuma ana ci gaba da tuntuɓa kan hanyoyin gyara halin da ake ciki.

“Muna tunanin cewa idan muka haɗa kai muka ci zaɓe, tabbas ƙasar za ta fuskanci sauyi,” in ji shi.

Da yake tunawa da lokacin da yake Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, Amaechi ya ce a wancan lokacin yara miliyan 10 ne ba sa zuwa makaranta, amma yanzu sun ƙara yawa.

Ya kuma nuna damuwa game da taɓarɓarewa tsaro a ƙasar.

“Rigimar manoma da makiyaya na nan, satar mutane don karɓar kuɗin fansa ma na ci gaba da faruwa,” in ji shi.

Amaechi ya alaƙanta matsalolin Boko Haram da sauran rikice-rikice da yunwa da matsin rayuwa.

“Na daɗe ina cewa Boko Haram ba rikicin addini ba ne. Da yawa daga cikin waɗanda ke ciki na shiga ne saboda yunwa da tsananin buƙata,” in ji shi.

Najeriya ta shafe sama da shekara 15 tana fama da rikicin Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas.

A watannin baya ma hare-haren mayaƙan sun ƙara tsananta, duk da iƙirarin gwamnati na cewa ta yi nasara.

Har ila yau, ’yan bindiga na ci gaba da addabar ƙauyuka a Zamfara, Sakkwato, Katsina da Kaduna, inda suka tilasta wa dubban manoma barin gonakinsu.

A cikin wani rahoton Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta Ƙasa, ta ce mutane 570 ne suka mutu a watan Afrilu 2025 kaɗai.

Wasu na ganin cewa ƙarfin siyasar Amaechi ya ragu, tun bayan rasa madafun iko musamman a Jihar Ribas.

Amma ya ƙaryata hakan.

“Ku je Fatakwal ku tambaya, daga filin jirgin sama ma, za ku ga ni da idonku,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
  • Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi
  • Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara
  •  Mutane 2 Sun Yi Shahada A Wani Harin HKI A Kudancin Kasar Lebanon