Ya ƙara da cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe zaɓe shi kaɗai.

“Ku bai wa Kudu tikitin, ku ga sakamako. Amma idan PDP ta ci gaba da tafiya a kan wannan kuskure, to, za ta fuskanci babbar matsala a 2027,” Yusuf ya bayyana.

Ya kuma bayyana cewa Atiku Abubakar ba ɗa  jam’iyyar PDP ba ne a yanzu, yana tare da wata sabuwar tafiyar haɗin gwiwa ta siyasa.

Yusuf ya ɗora alhakin faɗuwar jam’iyyar a zaɓen 2023 kan rashin kyakkyawan shugabanci da kuma rabon tikiti ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce rikicin cikin gida da kuma gazawar PDP wajen kulawa da ‘yan Kudu ne suka sa jam’iyyar ta faɗi.

Ya kuma nuna takaicinsa game da sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta na baya, Ifeanyi Okowa, zuwa jam’iyyar APC, yana mai cewa hakan na nuna cewa PDP ta kasa tsara kamfen ɗinta yadda ya dace.

Ya buƙaci shugabannin PDP da su daina dogaro da tsofaffi a siyasa, su mayar da hankali wajen gina sabuwar amana da haɗin kai, musamman a yankin Kudu.

A cewarsa, adalci, haɗin gwiwa, da sake gina jam’iyya su ne kawai hanyar da PDP za ta iya dawowa da ƙarfi a zaɓen 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi da ƙoƙon kanta

An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje.

Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin.

Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar.

A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu.

Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato

A ranar 19 ga Yuli, 2025 ne jami’an ’yan sanda suka kama wannan gungun mutane da kai a otel ɗin Bida.

Babban wanda ake zargin ya tabbatar cewa kan kakarsa ce mai shekaru sama da 90 a lokacin da ta rasu kimanin shekaru biyu da suka gabata.

Ya ce da farko ya samo kan ne bisa umarnin wani boka, don neman kuɗi cikin hanzari. Amma, bayan jin sharuddan tsafin, ya kasa bi, sai ya ɓoye kan na tsawon shekaru biyu.

Daga baya, abokinsa da wani kuma sun yi masa tayin sayenkan a kan Naira 100,000, kuma suka biya Naira 40,000 a matsayin kuɗin kafin alƙalami.

Daga nan suka kai wani wanda ake zargi da ninka kuɗi, da ya nemi Naira 500,000 don yin tsafin kuma sun biya shi da kaɗan-kaɗan.

Bayan an gama aikin, ya umarce su kada su buɗe ganga har sai ya gaya musu.

Makonni sun shude babu labari ko kuɗi sai suka yi masa takakkiya zuwa gidansa, amma ya shawo kansu cewa su haɗu a wani otel a Bida inda za su karɓi kuɗinsu.

A otel din ne kuma ’yan sanda suka kama su gaba ɗayansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
  • LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman
  • Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi da ƙoƙon kanta
  • ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
  • Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • An Watse A Taron EU Da China Saboda Ricikin Kasuwanci Da Siyasa  Tsakaninsu
  • Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu
  • Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu