A wasu lokuta, matsalolin suna fitowa kai tsaye sakamakon rashin fahimta daga mataki na kasa, wadada a wasu lokutan ba su da wata alaka da sakatariyar jam’iyyun da ke mataki na sama.

Ko a cikin jam’iyyar APC da ke mulki, akwai jayayya a cikin rassan jihohinta da ba su warware ba kuma suna barazanar ga damar jam’iyyar a jihohin da abin ya shafa.

Wasu masana harkokin siyasa sun bayyana cewa rarrabuwar kawunan ta samu ne sakamakon nuna iko tsakanin wasu mutane a wasu jihohi. Akwai batun wanda ke da iko da tsarin jam’iyyar shi ne shugaban jam’iyyar a jihar.

Yayin da wasu ke cewa wannan shi ne tushen da ya haifar da rarrabuwar kawuna da ke faruwa a cikin tsarin jam’iyyun a jihohi, inda jiga-jigan ‘yan siyasa ke ta kokarin mallakar masu ruwa da tsaki na jam’iyya ta yadda za sus amu damar kulawa da jam’iyyun a jihohinsu.

Masana harkikin siyasa na ganin cewa idan har abubuwa ba su Sanya ba, to za a fuskanci matsaloli a tsakanin mambobin jam’iyya a lokacin zaben fid da gwani, wanda hakan na iya shafar zaben 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Gwamna Umo Eno na Jihar Akwa Ibom, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Ya bayyana hakan ne a hukumance a ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar da ke Uyo, babban birnin jihar.

Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda

Wannan mataki ya biyo bayan wasu kwanaki da ya shafe yana nuna sha’awarsa na sauya sheƙa.

A wani taron jama’a da aka gudanar a Ikot Abasi, ya ce: “Lokaci ya yi da za mu motsa” domin a haɗa kai da Gwamnatin Tarayya da jam’iyyar APC ke jagoranta.

Gwamnan ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan shafe watanni uku yana tattaunawa da manyan mutane da masu ruwa da tsaki a jihar.

Ya nuna godiyarsa ga PDP saboda goyon bayan da suka ba shi, amma yanzu lokaci ya yi da zai ci gaba da tafiya gaba.

Ya bayyana cewa yana matuƙar ƙaunar Shugaba Bola Tinubu, kuma yana ganin Jihar Akwa Ibom za ta fi amfana idan tana aiki kafaɗa da kafaɗa da Gwamnatin Tarayya.

Gwamna Eno, ya sha alwashin cewa zai ci gaba da yi wa mutanen jihar aiki tuƙuru, ko daga wacce jam’iyya yake.

“Na kammala ganawa da jama’a a matsayin wanda kuka zaɓa, kuma na yanke shawarar komawa jam’iyyar APC,” in ji shi.

Gwamnonin jam’iyyar APC ne suka tarbe shi, ciki har da Gwamnan Jihar Imo kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Hope Uzodimma; Bassey Otu na Jihar Kuros Riba; Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas; da Dapo Abiodun na Jihar Ogun.

Sauran da suka halarta sun haɗa da Gwamna Sheriff Oborevwori na Delta, Monday Okpebholo na Edo, da Francis Nwifuru na Jihar Ebonyi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma
  • Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu
  • 2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
  • Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom
  • Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
  • Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC
  • Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
  • Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa
  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)