A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote
Published: 10th, June 2025 GMT
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan ba da jimawa ba al’ummar Nijeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.
Dangote ya bayyana hakan ne yayin ganawa da manema labarai, a lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa da ke yankin Lekki a Jihar Lagos.
Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne kaɗai, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.
“A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya ba mu ƙarin makamashi, ina mai shaida muku cewa nan ba da jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba kaɗai.”
A watan Oktoban bara ne dai Matatar Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a ƙasar.
To sai dai dillalan man fetur a Nijeriya, na ganin ya kamata Matatar Dangoten ta riƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote
এছাড়াও পড়ুন:
Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya
Koda ya ke dai, a lokacin ‘yansanda sun yi nisa ban gudanar bincike, amma babu wanda suka iya kamawa, kuma ba a kara shigar da wata sabuwar kara a gaban kotu ba, duk tsawon wadannan shekarun.
Wannan bukatar da Muyiwa ya biro da ita, tamkar bude wani sabon babi ne, kan batun hallaka manyan mutane a kasar, wadda za a iya cewa, tun daga 1999, har zuwa yau, amma shiru ake ji, kan daukar wani kwakwaran mataki.
A wani taro a kwanan baya, babban Lauya SAN Cif Kanu Agabi, ya bijiro da zargin yadda ake gaza hukunta masu aikata manyan laifuka a kasar, inda kuma ake samun dogon jan kafa, kan shari’ar da ta shafi, marasa karfi a kasar.
Wannan zargin na Kanu, ya nuna a zahiri, yadda aka yiwa bangaren shari’ar kasar, rikon Sakainar Kashi, musamman wajen gaza cafko, masu aikata manyan laifuka, domin su fuskanci hunci.
Bugu da kari, a kasidar da ya gabatar a a taron jamia’r NOUN, tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa, yin gaskiya wanzar da zaman lafiya tabbatar da tsaro, tare da bai wa ko wanne dan kasa hakkinsa, su ne, ginshikin da ke bunkasa tattalin arzikin kasa.
Sai abin dubi a nan, wannan yawabin na, Cif Olusegun, ya kasance yana cin karo da juna, domin a lokacin yana kan Karagar shugabancin kasar ne, aka kashe marigayi Ige.
Cafko irin wadannan masu halka manyan mutane a kasar domin a hukunta su, kamar yadda dokar kasa ta tanada, ba wai kawai hakan zai samar da salama ga ahalinsu bane, musamman duba da yadda suka yi babban rashi, amma hakan zai kuma zama wani babban abin ci gaba, ga kasar.
Kazalka, kamo su din, zai zama tamkar wani gargadi ne, da zai nuna cewa, akwai hukuncin da kasar ta tanadar, ga masu aikata irin wannan halin na rashin imani.
A nan, wannan Jaridar, ta yi waiwaye kan kisan rashin imani da aka akatawa mataimakin shugaban PDP na shiyyar Kudu Maso Kudu Cif Aminasoari Kala (A.K) Dikibo shekaru 21 da suka gabata.
Abin takaici, an hallaka shi ne, da tsayiyar rana a kan wata babbar hanya, a ranar ga 4 Fabiraurun 2004.
Sai dai, har zuwa yanzu, babu wani kokari da rundunar ‘yansanda ko hukumar DSS suka yi, na bankado makasan.
Kazalika, tshohon mataimakin shugaba na Kudu Maso Kudu, rusasshiyar jami’iyyar ANPP Marshal Sokari Harry, an kashe shi a Abuja a ranar 5 ga watan Maris na 2003 a lokacin zaben shugaban kasa
Hakazalika, an yiwa dan siyasa Anthony Olufunsho Williams, kisan gilla a gidansa da ke a rukunin gidaje na Dolphin, a jihar da ke Ikoyi, Legas, a ranar 27 ga watan Julin 2005.
An hallaka shi ne, yayin da ake shirin tsayar da shi, dan takarar gwamna a PDP na jihar Legas.
Rashin daukar matakin, na kara zubur da kimar Nijeriya a idon duniya.
Hakazalika, hakan ya sanya, wasu hukumomin a jihohin kasar nan, ke shawartar alumomin, da su dauki matakan kare kansu, daga hare-haren da aka kai wa jama’a, wanda hakan karara, ya nuna gazawar gwamnatin kasar, na kare rayuka da kuma dukiyoyin ‘yan kasar.
A saboda haka, akwai bukatar, a yiwa bangaren shari’a na kasar garanbawul, domin a lalubo da mafita kan lamarin.
Ko da yake dai, majalisar kasa na kan yunkurin sabunta dokar zabe ta 2022.
A matsayin mu a wannan Jaridar, mun kasance kan gaba wajen yin kira da a samar da sauye-sauye a bangaren shari’a, musamman domin a dawo da kimar da bangaren yake da shi, kamar yadda aka san shi, a shekarun baya.
A tunanin mu, samar da wannan sauye-sauyen a bangaren shari’ar, za a samar da kyakyawan yanayi a bangaren na shari’a, tare da gaggawar daukar makai, kan irin wannan kisan gillar da ake yiwa manyan kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp