Aminiya:
2025-06-11@20:37:35 GMT

A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote

Published: 10th, June 2025 GMT

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan ba da jimawa ba al’ummar Nijeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne yayin ganawa da manema labarai, a lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa da ke yankin Lekki a Jihar Lagos.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne kaɗai, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

“A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya ba mu ƙarin makamashi, ina mai shaida muku cewa nan ba da jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba kaɗai.”

A watan Oktoban bara ne dai Matatar Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a ƙasar.

To sai dai dillalan man fetur a Nijeriya, na ganin ya kamata Matatar Dangoten ta riƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba Zaɓen 2027 ba — ACF

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Nijeriya ACF ta bukaci Shugaba Bola Tinubu da manyan muƙarraban gwamnatinsa da su daina gaggawar shige-da-fice wajen neman tazarce a Zaɓen 2027.

ACF ta ce zai fi dacewa gwamnatin Tiinubun ta mayar da hankali wajen ganin ta kyautata rayuwar ’yan Nijeriya maimakon gangamin yaƙin neman a sake zaɓensa a 2027, lamarin da ƙungiyar cewa hakan ya yi wuri.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba Ɓarawon waya ya kashe babban jami’in soja da wuƙa a Kaduna

Wannan kira dai na kunshe cikin wata sanarwar yi wa musulmi barka da Sallah Babba da kakakin ƙungiyar na ƙasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba ya fitar.

Ƙungiyar ta bayyana rashin jin daɗinta dangane da taɓarɓarewar tsaro da tsadar rayuwa da rashin wutar lantarki da matsalolin lafiya, ilimi da karyewar darajar Naira da tashin farashin kayan abinci.

Ƙungiyar ta kuma nuna takaicinta yadda duk da irin waɗannan ƙalubale amma jam’iyyar APC ta fi mayar da hankali kan gangamin yaƙin neman zaɓen Tinubun a 2027.

Ana iya tuna cewa a watan da ya gabata ne dukkanin gwamnonin jam’iyyar APC 22 a faɗin ƙasar suka amince da cewa Bola Tinubu ne ɗan takararsu a zaɓen 2027 mai zuwa, lamarin da ake ci gaba cece-kuce a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu
  • Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Harkar Man Fetur Za Ta Sauya A Nijeriya – Dangote
  • Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi
  • Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya
  • A saurari sauyin da mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote
  • Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike
  • Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha
  • Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba Zaɓen 2027 ba — ACF