Aminiya:
2025-06-12@08:50:34 GMT

A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alou — Gwamnatin Borno

Published: 11th, June 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Borno ta yi kira ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta hanzarta ɗaukar mataki kan ɗan kwangilar da ta baiwa aikin yashe dam ɗin Alou da ya haifar da ambaliya a bara.

Ta ce duk da cewar sun yashe wani sashe na dam din amma, har yanzu akwai babbar barazana da za a iya fuskantar mummunar ambaliya.

Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin tsaro na Jihar Borno, Farfesa Umar Tar da harkokin tsaro ya shaida wa BBC cewa an bayar da kwantaragin kuma minista ya je ya ƙaddamar da aikin.

“Har yanzu ba mu ga ’yan kwangila sun zo domin fara aikin ba kuma yanzu ga damuna ta riga ta sauka.

“Idan ba a yi aikin nan da wuri ba to idan ruwa ya zo ya yi halinsa to lallai za a samu matsala.

“Ya kamata a ce an yashe ruwan saboda irin cunkushewar da ya yi. Idan aka yashe shi to ko ruwa ya zo da yawa ba zai ambaliya ba,” in ji Farfesa Tar.

A damunar bara ne dai madatsar ruwa ta Alou Dam ta cika ta tunbatsa inda ta kuma karye, wani abu da ya janyo ambaliyar ruwa da ya haddasa asarar rayuka da ta dukiyoyi a birnin Maiduguri.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno Madatsar Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa, a halin yanzu Jamhuriyar Musulunci za ta iya kai wa Isra’ila hari “daidai” inda ta ke so bayan samun bayanan sirri kan cibiyoyin nukiliyar gwamnatin Isra’ila.

Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wata wasika mai zuwa ga ministan leken asirin kasar, Esmail Khatib, inda ya taya shi murnar wani samame da aka kai a kwanan baya wanda ya bayar da damar samun bayyana sirrin Isra’ila da dama kan shirinta na nukiliya.

Wannan nasarar, ta baiwa hukumomin leken asirin Iran damar samun wasu tarin takardun Isra’ila da suka shafi makaman nukiliya, soji, tsaro da wasu wurare na kayayyakin more rayuwa.

Wuraren sun hada da wuraren da Isra’ila ke da shirin nukiliyar gwamnatin na boye, wanda aka ce ya baiwa Tel Aviv damar kera daruruwan makamai masu linzami da ba a san da su ba.

Janar Salami ya kara da cewa: “Wadannan takardun sirrin babu shakka zasu inganta tasirin kokarin da ake yi na hanzarta kawar da gwamnatin Sahayoniyawan da kuma kara sahihancin harin makamai masu linzami na Iran.

A shekarar da ta gabata Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kai hari kan wasu muhimman wurare na Isra’ila a yankunan Falasdinawa da ta mamaye a wani gagarumin farmakin ramuwar gayya da ta gudanar a matsayin mayar da martani ga wuce gona da iri na gwamnatin Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
  • A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alau — Gwamnatin Borno
  • Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa
  • Gidauniyar Hind Rajab ta kai karar Isra’ila kan harin jirgin ruwan Madleen
  • IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so
  • Gwamnatin Borno Ta Nemi A Gaggauta Yashe Alo Dam Don Guje Wa Sabuwar Ambaliya
  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza
  • Wasu Jiragen Ruwa Na  Ceto Da Jin Kai  Sun  Tashi Daga Tunisiya Zuwa Gabar Ruwan Gaza