Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya
Published: 11th, June 2025 GMT
Kasashen Sin da Kenya sun zurfafa hadin gwiwarsu a bangaren kiwon lafiya, inda kasar Sin ta bayar da guraben tallafin karatu 500 da kaddamar da shirye-shiryen musaya 20 a kwacce shekara.
Wata sanarwa da aka fitar bayan taron da aka yi tsakanin jakadar Sin dake Kenya Guo Haiyan da babban sakataren ma’aikatar lafiya ta kasar Aden Duale, ta ce hadin gwiwar kasashen biyu na da muhimmanci wajen kyautata makomar kasar ta zama jagora a bangaren kiwon lafiya.
A cewar Adel Duale, bangarorin biyu sun kuma tattauna game da kafa cibiyoyin samar da riga kafi da harhada magunguna ta hanyar amfani da fasahar kasar Sin.
Ya kara da cewa, shirin hadin gwiwa na dala miliyan 500 a tsakaninsu zai mayar da hankali wajen karfafa tsarin samar da kayayyaki a kasar Kenya da rage dogaro kan shigar da kayayyaki daga ketare da samar da guraben ayyukan yi da kai kasar ta gabashin Afrika matsayin jagora a fannin samar da kayayyakin kiwon lafiya. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
A yau ne aka gudanar da taron ministoci masu daidaita ayyukan da aka amince, a gun taron tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, a birnin Changsha dake lardin Hunan na kasar Sin, inda ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci bikin kaddamar da taron, tare da karanta wasikar murnar bude bikin ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana ministan harkokin wajen kasar Kongo Brazaville Jean-Claude Gakosso, ya karanta wasikar murnar bude bikin ta shugaban kasarsa Denis Sassou Nguesso. Taron ya samu halartar ministocin kasashe membobin kungiyar FOCAC, da wakilan kwamitin AU, da jakadun kasashen Afirka dake kasar Sin, wadanda adadinsu ya zarce 100.
Wang Yi ya jaddada cewa, ya kamata Sin da Afirka su nuna goyon baya ga juna, da tabbatar da hadin kai a tsakanin kasashe masu tasowa a duniya, da ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da yin kira da rika gudanar da cinikayya cikin ‘yanci a duniya, da ci gaba da samun moriyar juna, da kiyaye hadin gwiwar kasa da kasa, da samun bunkasuwa tare, da kiyaye adalci da tabbatar da odar kasa da kasa, da yin mu’amala da juna, da kuma sa kaimi ga tabbatar da bambance-bambancen wayewar kan duniya.
Minista Gakosso ya wakilci kasashen Afirka, inda ya bayyana cewa, ana maraba da shirye-shirye 10, na raya dangantakar abokantaka da shugaba Xi Jinping ya gabatar, da nuna goyon baya ga fatan hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2035, tare da fatan za a aiwatar da ayyukan da aka amince da su, a gun taron kolin FOCAC na birnin Beijing.
A hannu guda kuma, bangaren Afirka ya bayyana adawa da matakan kara buga harajin kwastam, da sanya takunkumi daga bangare daya, yana tsayawa tare da kasar Sin wajen tinkarar kalubale bai daya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp