Aminiya:
2025-06-13@16:30:33 GMT

Leroy Sane ya koma Galatasaray

Published: 13th, June 2025 GMT

Kungiyar kwallon kafa ta Galatasaray a wannan Alhamis din ta sanar da daukar dan wasan Jamus, Leroy Sane daga Bayern Munich.

Kungiyar ta Turkiyya ta dauki dan wasan ne kyauta bayan kwantaraginsa ya kare a Munich.

Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane

Sane mai shekaru 29 ya rattaba hannu kan kwantaragin shekaru uku inda zai rika daukar albashin Yuro miliyan 9 — kwantankwacin Dala miliyan 10.

4 — duk shekara kamar yadda kulob din bayyana.

Sane ya buga wa kasarsa ta Jamus wasanni 70, inda kuma ya lashe kofunan Bundesliga guda hudu a Bayern Munich tun bayan raba gari da Manchester City, inda ya dauki Firimiyar Ingila guda biyu.

A kakar bana Sane ya jefa kwallaye 13 a duk gasannin da ya haska, inda ya taimaka wa Bayern lashe gasar Bundesliga bayan ta subuce daga hannunta a kakar bara.

 

AFP

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayern Munich Galatasaray

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka ba tare da taɓarɓarewa nan da shekaru uku masu zuwa.

Bankin ya yi hasashen haɓakar ma’aunin tattalin arzikin cikin gida, GDP da kashi 3.6 cikin 100 a shekarar 2025, sai kashi 3.7 a shekarar 2026 da kuma kashi 3.8 a shekarar 2027.

Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci

A cewar sabon rahoton tattalin arzikin duniya da Bankin ya fitar, ana sa ran za a tallafa wa matsakaicin lokaci na Nijeriya ta hanyar samar da ingantattun albarkatun mai, da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi, da kuma farfado da ƙwarin gwiwar masu zuba jari.

Rahoton ya yi nuni da cewa, yayin da tattalin arzikin kasar ke shirin fadada, kalubale irin su hauhawar farashin kayayyaki, da matsalar canjin kudi, da kuma gibin kasafin kudi na ci gaba da zama babbar barazana ga ci gaba mai ɗorewa.

Bankin ya kuma kara da cewa, aiwatar da sauye-sauye a fannin tattalin arziki da gwamnatin Nijeriya ke yi, musamman ta fuskar farashin makamashi da tattara kuɗaɗen shiga, da sarrafa kuɗaɗen musaya, zai taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da waɗannan hasashen ci gaban.

Ana sa ran ci gaban Nijeriya a shekarar 2025 zai kasance matsakaici da kashi 3.3 cikin 100, yayin da matsalolin tsarin ke ci gaba da yin la’akari da saurin farfadowar tattalin arziki.

Bankin Duniya ya yi kira ga masu tsara manufofin Nijeriya da su ba da fifiko ga sauye-sauyen tsarin da ke inganta ci gaban kamfanoni masu zaman kansu, inganta ababen more rayuwa, da inganta jarin ɗan Adam don ɗorewar bunkasar tattalin arziki na dogon lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya
  • Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Tawagar Fursininin Yaki Na Rasha Sunn Koma Gida Daga Kieve
  • IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so