Ya ce dukkan wadanda aka sacen, da suka hada da mata 9 da maza 2, an kubutar da su ba tare da wani rauni ba.

PPROn ya bayyana cewa, a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don ganowa tare da cafke ‘yan bindigar da suka tsere, inda rundunar ‘yansandan ta sha alwashin ci gaba da matsa lamba kan masu aikata laifuka a jihar.

ceto mutane 11 da aka yi garkuwa da su a Katsina

 

 

Rundunar ‘yansandan jihar Katsina tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro sun yi nasarar ceto mutane 11 daga hannun masu garkuwa da mutane a daren Lahadi 8 ga watan Yuni 2025.

 

Wannan nasarar an sameta ne da misalin karfe 10:30 na dare a hanyar kauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a karamar hukumar Danmusa biyo bayan wani sintiri da rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro ke yi a hanyar.

 

Tawagar ta hada da jami’an ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Operation Sharan Daji, da hukumar kula da al’umma ta jihar Katsina (KSCWC), da kuma ‘yan banga na yankin.

 

A cewar wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya fitar, ta ce rundunar tsaron ta ci karo da wasu gungun ‘yan bindiga da ke yunkurin tserewa da wadanda suka sace daga sassa daban-daban na jihar.

 

Aliyu ya bayyana cewa, an yi musayar wuta, wanda ya tilastawa ‘yan bindigar tserewa tare da barin wadanda suka yi garkuwa da su a dajin.

 

Ya ce dukkan wadanda aka sacen, da suka hada da mata 9 da maza 2, an kubutar da su ba tare da wani rauni ba.

 

PPROn ya bayyana cewa, a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don ganowa tare da cafke ‘yan bindigar da suka tsere, inda rundunar ‘yansandan ta sha alwashin ci gaba da matsa lamba kan masu aikata laifuka a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya ne ga ‘yan mamayar Isrta’ila

Jami’in kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bayyana cewa: Kamen da jami’an tsaron Hukumar Falasdinawa suka yi na wani gungun ‘yan gwagwarmaya a Nablus da Jenin, da kwace makamansu, da kuma ci gaba da fatattakar ‘yan gwagwarmaya a duk fadin yankin gabar yammacin kogin Jordan, yana nuni da ci gaba da goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila ce da murkushe al’ummar Falastinu.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, Shadid ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa: Kamen da jami’an tsaron hukumar cin gashin kan Falasdinawa suka yi kan ‘yan gwagwarmaya da kuma fitattun al’umma da masanan Falasdinawa, biyan ladar moro-maron yahudawan sahayoniyya ne da jami’an hukumar Falasdinu suka ci.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ruguza gidajen mutane a Jenin, tare da koran dubban mutane a Tulkarm, ana kuma kwace yankunan mutane a gabar yammacin kogin Jordan.

Shadid ya bayyana cewa: Wadannan ayyuka suna nuna manufar Hukumar Cin gashin Falasdinawa ne na ganin ta raba ‘yan gwagwarmaya da yankin gabas yammacin kogin Jordan, tare da barin Falasdinu a bude ga sojojin mamayar Isra’ila gungun ‘yan ta’addan su aiwatar da tsare-tsaren Sanya Falasdinawa gudun hijira.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi