Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Published: 9th, June 2025 GMT
Ya ce dukkan wadanda aka sacen, da suka hada da mata 9 da maza 2, an kubutar da su ba tare da wani rauni ba.
PPROn ya bayyana cewa, a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don ganowa tare da cafke ‘yan bindigar da suka tsere, inda rundunar ‘yansandan ta sha alwashin ci gaba da matsa lamba kan masu aikata laifuka a jihar.
ceto mutane 11 da aka yi garkuwa da su a Katsina
Rundunar ‘yansandan jihar Katsina tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro sun yi nasarar ceto mutane 11 daga hannun masu garkuwa da mutane a daren Lahadi 8 ga watan Yuni 2025.
Wannan nasarar an sameta ne da misalin karfe 10:30 na dare a hanyar kauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a karamar hukumar Danmusa biyo bayan wani sintiri da rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro ke yi a hanyar.
Tawagar ta hada da jami’an ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Operation Sharan Daji, da hukumar kula da al’umma ta jihar Katsina (KSCWC), da kuma ‘yan banga na yankin.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya fitar, ta ce rundunar tsaron ta ci karo da wasu gungun ‘yan bindiga da ke yunkurin tserewa da wadanda suka sace daga sassa daban-daban na jihar.
Aliyu ya bayyana cewa, an yi musayar wuta, wanda ya tilastawa ‘yan bindigar tserewa tare da barin wadanda suka yi garkuwa da su a dajin.
Ya ce dukkan wadanda aka sacen, da suka hada da mata 9 da maza 2, an kubutar da su ba tare da wani rauni ba.
PPROn ya bayyana cewa, a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don ganowa tare da cafke ‘yan bindigar da suka tsere, inda rundunar ‘yansandan ta sha alwashin ci gaba da matsa lamba kan masu aikata laifuka a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.