Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Inganta sinadarin Uranium da ɗage takunkumai na iya sa tattaunawar ta yi amfani

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta cewa: A bayyane yake cewa cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da zaman lafiya na dindindin na shirin makamashin nukiliyar Iran abu ne mai yiyuwa, kuma ana iya cimma shi cikin sauri.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta a shafinsa na Twitter game da sabon zagayen tattaunawa tsakanin Iran da Amurka da kuma matsayin Iran a kansu yana mai cewa: Shugaba Trump ya bayyana a lokacin da ya shiga fadar White House cewa ba lallai ne Iran ta mallaki makamin nukiliya ba, wannan matsayi ya yi daidai da akidar Iran ta nukiliya, kuma za a iya la’akari da shi a matsayin tushen yarjejeniyar da za a iya cimmawa.

Ya kara da cewa: A yayin da ake ci gaba da tattaunawa a ranar Lahadi, a bayyane yake cewa yarjejeniyar da za ta tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a shirin nukiliyar Iran na kan hanya, kuma za a iya cimmawa cikin gaggawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Babban Darektan Hukumar IAEA Saboda Yadda Yake Mika Wuya Ga Bakar Siyasa

Babban darektan hukumar IAEA ya zama tamkar wata yar tsana ce a hannun kasashen Yamma don dakile shirin nukiliyar Iran

An fara taron kwata-kwata na hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa a birnin Vienna, wanda ya samu halartar wakilan kasashe 35 mambobi hukumar

Bisa la’akari da rahoton da babban daraktan ya fitar game da sa ido da tabbatar da shirin nukiliyar Iran karkashin yarjejeniyar kare kai da kuma tsarin aiwatar da ayyukan hadin gwiwa ta (JCPOA) na daya daga cikin batutuwan da za a tattauna.

Babban darektan hukumar ta IAEA Rafa’el Grossi ya sanar a wani rahoto da ya fitar a makon da ya gabata cewa; Yawan sinadarin uranium da Iran ke da shi ya ninka har kashi 60 cikin dari. Kamar yadda ya yi zargin samuwar wata makamashin nukiliya da Iran ba ta bayyana ba a baya, yana mai nanata batutuwan da aka rufe a baya a cikin matsalar da ya shafi harkar soji (PMD) tun a shekara ta 2015.

A martanin da Iran ta mayar a hukumance ta nuna rashin amincewarta da rahoton, inda ta bayyana shi da cewa ya kaucewa aikin fasaha na hukumar IAEA da kuma Sanya batun siyasa da nuna son kai. A cikin wata sanarwa da hukumar ta IAEA ta Iran ta aikewa hukumar ta IAEA ta duniya, ta yi watsi da wadannan zarge-zargen, tare da tabbatar da cewa babu wasu ayyukan nukiliya da ba a bayyana ba a kasar Iran, kuma shirin nukiliyar kasar na da cikakken gaskiya kuma yana karkashin kulawar hukumar ta IAEA ta duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Sake Tunzura Iran Shirin Makamashin Nukiliyarta Zai Fuskanci Martani
  • He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha
  • Iran: Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Tace Zata Maida Martani Kan Hukumar IAEA
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Tace Sinadarin Uranium
  • Jami’in Makamashin Nukiyar Iran Ya Ce; Zarge-Zargen Da Ake Yi Kan Shirin Makmashin Nukiliyar Iran Siyasa Ce Kawai
  • Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Babban Darektan Hukumar IAEA Saboda Yadda Yake Mika Wuya Ga Bakar Siyasa
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza