Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Inganta sinadarin Uranium da ɗage takunkumai na iya sa tattaunawar ta yi amfani

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta cewa: A bayyane yake cewa cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da zaman lafiya na dindindin na shirin makamashin nukiliyar Iran abu ne mai yiyuwa, kuma ana iya cimma shi cikin sauri.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta a shafinsa na Twitter game da sabon zagayen tattaunawa tsakanin Iran da Amurka da kuma matsayin Iran a kansu yana mai cewa: Shugaba Trump ya bayyana a lokacin da ya shiga fadar White House cewa ba lallai ne Iran ta mallaki makamin nukiliya ba, wannan matsayi ya yi daidai da akidar Iran ta nukiliya, kuma za a iya la’akari da shi a matsayin tushen yarjejeniyar da za a iya cimmawa.

Ya kara da cewa: A yayin da ake ci gaba da tattaunawa a ranar Lahadi, a bayyane yake cewa yarjejeniyar da za ta tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a shirin nukiliyar Iran na kan hanya, kuma za a iya cimmawa cikin gaggawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha                                                                                                                                                                     

Mai ba da shawara ga Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayyana cewa: Hanyar Zangezur wata shiri ne na Amurka don matsawa kasashen Rasha da Iran.

Ali Akbar Velayati mai ba wa Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran shawara kan harkokin kasa da kasa, ya dauki aikin Zangezur (arewa maso yammacin Iran) a matsayin wani aikin Amurka na matsawa kasashen Rasha da Iran lamba.

A cikin wani sako na tunawa da Sheikh Safi al-Din Ardebili, Velayati ya yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi Azarbaijan da mashigar Zangezur, yana mai cewa, “Makiya Iran karkashin jagorancin ‘yan sahayoniyyan duniya da Amurka, suna neman ta hanyar tsare-tsare irin su mashigar Zangezur, don ciyar da manyan ayyukan siyasa a karkashin fakewa da wadannan tsare-tsare.”

Ya kara da cewa, manufar farko ita ce raunana gwagwarmaya da yanke  alakar Iran da yankin Caucasus da kuma killace Iran da Rasha ta kasa a kudancin yankin.

Ya bayyana cewa: “Wannan aikin ba wai kawai wani bangare ne na shirin Amurka na maye gurbin Ukraine da yankin Caucasus a matsayin wani sabon fage na matsin lamba kan Rasha da Iran ba, amma ana aiwatar da shi ne tare da goyon bayan kungiyar tsaro ta NATO da kuma wasu kungiyoyin ‘yan kishin kasa na Turkiyya (Pan-Turkist).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  •  Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha                                                                                                                       
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha                                                                                                                                                                     
  • Iran Da Afganistan Sun Tattauna Dangane Da Komawar Afganawa Gida
  • Kasar Iran Ta Ce Tana Hulda Da Amurka Ta Hanyar Masu Shiga Tsakani
  • Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
  • Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
  • Araqchi Ya Jaddada Cewa; Karfin Kariya Da Makamai Masu Linzamin Iran Ne Suka Tilastawa Makiya Neman Tsagaita Wuta