Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta bayyana cewa; Matakin da Amurka ta dauka na kakaba takunkumin  shiga Amurka akan wasu ‘yan kasa da kuma wasu kasashen musulmi yana nuni da yadda Amurkan take adawa da musulmi.

Haka nan kuma ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta ce; Daukin matakin hana wasu mutane yin tafiya saboda  kasar da su ka fito, ko addininsu yana nuni ne da yadda Amekin take jin fifiko da kuma nuna wariya.

A karshe ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta yi kira ga MDD da sauran cibiyoyin kasa da kasa na shari’a da su dauki mataki karara kuma a fili akan abinda Amurka ta yi, da ya sabawa duk wani ma’auni na ‘yan adamtaka.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya rattaba hannu akan wata doka wacce ta hana ‘yan kasashe 12 shiga cikin Amurka, da kuma kafa tarnaki  akan wasu ‘yan kasashen 7. Fadar White House ta Amurka ta bayyana wannan matakin da ta dauka akan cewa; manufarsa shi ne kare tsaron kasar Amurka.

Kasashen da takunkumin shiga Amurkan ya shafa sun hada Afghanistan, Myanmar, Chadi, DRC, Equatorial Guinea, Eritria, Iran, Libya, Somaliya, Sudan da Yemen.

Su kuwa wadanda aka yi msu tarnaki ,sun kunshi  Brundi, Cuba, Laos, Saliyo, Togo, Turkimanestan da kuma Venezuela.

Shugaban na kasar Amurka ya kuma kara da cewa; Abu ne mai yiyuwa anan gaba a kara shigar da wasu kasashen.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

Barcelona ta amince da yarjejeniyar ɗaukar ɗan wasan gaba na ƙungiyar Athletic Bilbao Nico Williams, amma kuma har yanzu akwai ƙalubalen da zasu fuskanta kafin ɗan wasan ya samu damar rattaba hannu a ƙungiyar ta Catalonia, ɗan wasan na ƙasar Sifaniya Williams, wanda ya zura ƙwallaye 31 a wasanni 167 da ya buga wa Bilbao, ya janyo hankalin ƙungiyoyin Arsenal da Bayern Munich a bana.

Amma ɗan wasan mai shekaru 22 ya amince da kwantiragin shekaru shida a Barcelona, wanda hakan zai sa ya hadu da abokinsa kuma abokin wasansa a matakin ƙasa Lamine Yamal a Nou Camp, Williams ya buƙaci Yamal da ya taimaka masa wajen zuwa Barcelona, bayan kakar da ya yi a Bilbao inda ya taimaka musu kai wa gasar zakarun Turai da kuma wasan kusa da na ƙarshe na gasar Europa duk a bana.

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona  Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Barcelona ta yi yunƙurin ɗaukar ɗan wasan Liverpool Luis Diaz a farkon bazara amma sai Liverpool ta nuna cewa darajar ɗan ƙasar Colombian ta kai fam miliyan 80, hakan ya sa Barca ta janye daga cinikin, Williams yana da yarjejeniyar da ta kai Yuro miliyan 62 (£53m) a kwantiraginsa a San Mames, wanda Barcelona ta nuna cewa za ta iya biya.

Daraktan wasannin Barcelona Deco ya gana da Williams da wakilansa a Ibiza a farkon wannan makon, inda aka amince da yarjejeniya ta fatar baki, Williams ne ya fara zura ƙwallo a raga a wasan ƙarshe na kofin European Cup da suka doke Ingila da ci 2-1 a Berlin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran
  • Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki