Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta bayyana cewa; Matakin da Amurka ta dauka na kakaba takunkumin  shiga Amurka akan wasu ‘yan kasa da kuma wasu kasashen musulmi yana nuni da yadda Amurkan take adawa da musulmi.

Haka nan kuma ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta ce; Daukin matakin hana wasu mutane yin tafiya saboda  kasar da su ka fito, ko addininsu yana nuni ne da yadda Amekin take jin fifiko da kuma nuna wariya.

A karshe ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta yi kira ga MDD da sauran cibiyoyin kasa da kasa na shari’a da su dauki mataki karara kuma a fili akan abinda Amurka ta yi, da ya sabawa duk wani ma’auni na ‘yan adamtaka.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya rattaba hannu akan wata doka wacce ta hana ‘yan kasashe 12 shiga cikin Amurka, da kuma kafa tarnaki  akan wasu ‘yan kasashen 7. Fadar White House ta Amurka ta bayyana wannan matakin da ta dauka akan cewa; manufarsa shi ne kare tsaron kasar Amurka.

Kasashen da takunkumin shiga Amurkan ya shafa sun hada Afghanistan, Myanmar, Chadi, DRC, Equatorial Guinea, Eritria, Iran, Libya, Somaliya, Sudan da Yemen.

Su kuwa wadanda aka yi msu tarnaki ,sun kunshi  Brundi, Cuba, Laos, Saliyo, Togo, Turkimanestan da kuma Venezuela.

Shugaban na kasar Amurka ya kuma kara da cewa; Abu ne mai yiyuwa anan gaba a kara shigar da wasu kasashen.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya

Shugaban kasar Iran Masuod Pezeshkiyan ya zanta ta wayar tarko tare da shugaban kasar Masar abdulfatta Assisi, inda suka taya juna murnar tahowar sallar Babba. Shugaban ya bayyana cewa kasar Iran tana da tsari ta makobta farko, don haka ne take, kara kyautata dangantaka da kasashe makobta da kuma musamman kasar ta Masar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a wata wayar tarho ta daban shugaban ya zanta da Yarima mai jiran gadon sarautan saudiya kuma Firay ministan kasar Muhammad bin Salman inda ya taya shi murnar zagayowar ranar Sallah babba sannan suka yi maganar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu. Duk tare da bambancin ra’ayin da kasashen biyu suke da shi dangane da yadda za’a warware matsalar falasdinawa kasashen biyu sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a gaza a kuma isar da kayakin agaji da gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Miliyoyim Musulmi A Nan Iran Da Sauran kasashen Duniya Ne Suka Yi Sallar Idin Layyah
  • Gwamnatin Kasar Chadi Ta Maida Martani Kan Dokar Hana Yan Kasar Shiga Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka