Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Published: 7th, June 2025 GMT
Yanzu mun yi hakan a kananan Hukumomi takwas,zuwa Lahadi mai zuwa,zamu je ta tare. Zamu ci gaba da yin hakan har zuwa watan Nuwamba wanda hakan zai sa mu kammala da kananan Hukumomi 27. Zuwa yanzu ana ganin amfanin abinda aka yi,a duk kananan Hukumomi da muka ziyarta. Ina ganin mun yi rawar gani kan muradai 12,amma kamar yadda na ce al’ummar Jigawa sune wadanda ya dace su yi bayani kan irin ayyukan alkhairi da ci gaban da muka yi a matsayinmu na gwamnati.
Da aka yi ma shi maganar ya ware kashi 30 cikin 100 saboda bangaren ilimi,cewa ya yi ai Jigawa Jiha ce da take da manoma. Domin kuwa kusan kashi 85 zuwa 90 na yawan al’ummar manoma ne. Duk wata gwamnatin da take bukatar bunkasa tattali arzikin Jigawa da kuma jin dadin zamantakewar al’ummarta dole ne ta maida hankali kan aikin noma. Fannin akin noma shi yake samar da kashi 46 cikin 100 kudaden shiga na gwamnati a shekara.Ina farin ciki na fadi hakan cewar abinda muke yi yayi matukar bunkasa tattalin arzikin Jihar Jigawa, Gaskiya daukar matakin yin hakan ko shakka babu ya bunkasa jin dadin rayuwra al’ummarmu. Maganar gaskiya tsarin ya rage yawan wadanda suke zuwa Birane daga Kauyuka a cikin Jihar. Matasa yanzu sun amince da harkar noma ita ce babbar lamarin kasuwanci amma ba irin noman da mutum zai noma saboda shi kadai ba.Shi yasa muka bada muhimmanci da maida hankali kan noma da komawa gona.
Shi kuma ilimi wani babban ginshikin ci gaban rayuwa ne, ta kowane al’umma na duniya,amma ba sai Jihar Jigawa kawai ba.Shi,yasa muke ganin da akwai muhimmanci da kuma bukatar mu ilimantar da al’ummar mu, saboda kuwa mun san da zarar mun ilimantar da su, musamman ma matasa,wadanda sune za su kasance Shugabannin gobe. Shi yasa lamarin ilimi ma shi ma muka bashi muhimmanci. Domin ai muna da tsare tsaren na lamarin daya shafi ilimin. A babban bangaren ilimin, mun kaddamar da tsarin da ya shafi kafar sadarwa ta zamani a ilmance,ba,abin ya tsaya a samar da ilimi ga al’ummar ba,abin ma yana taimaka mana kan lamarin rashin zuwa aiki na Malaman makaranta.
Bugu da kari an amfana da shi wajen horon su Malaman.Zuwa yanzu,mun haorar da fiye da Malaman makaranta12,a karkashin shi tsarin.
Hakanan ma mun bullo da tsari na rage yawan yaran da basu zuwa makaranta, shi yasa ma muka bullo da tsarin Tsangaya, saboda kuwa Hukuma ce wadda ta fara aiki.Abinda muke yi shi ne mu tabbatar da duk yara a Jihar Jigawa,wadanda basu zuwa makaranta, an dawo da su makaranta.Mun samu nasrara yin hakan.Tsarin Tsangaya ya amince da masu ruwa da tsaki za a koyar da abubuwa uku:lamarin kirga da kuma yakar jahilci na kwana biyu,ilimin addii na kwana uku,sai kuma ilimin koyon sana’a na kwana daya.Tsarin makaranta na Tsangaya zai bada dukkannin abubuwan da suka zama dole wadanda kuma za su taimakawa masu karatu wajen samar da ilimin fasaha da kuma koyon sana’oi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu
Wani Lauya Okere Kingdom Nnamdi, wanda ya gabatar da takardu don samun rajistar Jam’iyyar Mutanen Kasa (PPP) a ranar 28 ga Maris, 2025, ya ce bayan wata daya sai INEC ta bayyana cewa ba ta bude adireshin fara yin rajistar sabbin jam’iyyun siyasa.
Jami’an INEC da suka yi magana kan lamarin, sun musanta zarge-zargen. Sun bayyana cewa duk da cewa an karbi bukatar yin rajista har guda 104, ana ci gaba da gudanar da bincike, sannan kuma tsarin zai fara gudana nan ba da dadewa ba ta hanyar sadarwaar zamani don inganta gaskiya da ingancin aiki.
“Hukumar ta amsa wa masu nema. Ba daidai ba ne a zargi INEC da jinkirin amsa bukatun yin sabbin rajistar. Za a bude Shafin intanet dazarar an kammala duk wani aikace-aikacen da suka cika ka’ida,” in ji wani babban jami’in hukuman.
Mai magana da yawun INEC, Rotimi Oyekanmi, ya sake jaddada cewa kungiyoyin siyasa dole ne su bi doka da oda na tsarin mulkin kasa kafin a yi musu rajista.
“Dole ne INEC ta tabbatar da cewa an bin doka. An bayyana ka’idojin, kuma har idan mai nema bai cika su ba, to ba za a iya masa rajistar ba har sai ya cika,” in ji shi.
Wani mai sharhi kan harkokin shari’a ya bayyana cewa jinkirin aiwatar da rajistar na iya kawo cikas ga shirin zabe, musamman ganin cewa ana sa ran fara zaben fid da gwani na jam’iyya a tsakiyar 2026.
Tsohon shugaban kungiyar siyasa ta kasa da kasa, Farfesa Adele Jinadu ya ce, “Idan masu nema sun bi ka’idojin kundin tsarin mulki da na zabe, babu wata kuntatawa ga rajistar jam’iyya a karkashin tsarin jam’iyyu masu yawa.”
Dakta Dauda Garuba na cibiyar ci gaban dimokiradiyya (CDD) ya kara da cewa, “Idan aka bai wa jam’iyyu damar gudanar da aikinsu cikin ‘yanci da zaman kansu, da yawa daga cikin kalubalen da muke fuskanta a yau ba za su taso ba.”
A ranar 6 ga Maris 2025 ne, majalisar wakilai ta amince da karatu na biyu kan kudirin dokar da ke neman canza rajistar da tsarin kula da jam’iyyun siyasa daga INEC zuwa wani sabon hukuma mai zaman kanta.
Kudirin hadin gwiwa tsakanin shugaban majalisan, Abbas Tajudeen da dan majalisa, Marcus Onobun, wannan kudurin na bayar da shawarar kafa kotun kula da takaddama tsakanin jam’iyyu don warware rikici cikin gida da rikice-rikicen tsakanin jam’iyyun.
An tura kudirin zuwa kwamitocin da ke kula da al’amuran zabe da kuma jam’iyyun siyasa don kara dubawa.
Duk da karuwar kiraye-kiraye na shiga harkokin siyasa, masu nazari da yawa na ganin cewa lokaci na kurewa ga sabbin jam’iyyun wajrn yi musu rajista yadda ya kamata da kuma shirya su kafin zaben 2027.
Shugaban jam’iyyar AA, Barrister Kenneth Udeze ya yi gargadin cewa, “Bai kamata a yi rajistar kowace jam’iyya ba kasa da watanni 12 kafin zabe. Bisa fatan gudanar da zaben fid da gwani na jam’iyyun a tsakiyar 2026, lokaci na kara kuantowa.
A halin yanzu, Nijeriya na da jam’iyyun siyasa 19 da aka tabbatar da rajistarsu, daga cikin 91 bayan INEC ta cire rajistar jam’iyya 74 a shekarar 2020 bisa ga rashin kwazonsu. Jam’iyyun da suka rage sun hada da APC, PDP, LP, NNPP, SDP, ADC, da sauransu.
Irin su, jam’iyyar matasa (YP) da jam’iyyar Boot (BP) sun sake samun rajista ta hanyar hukuncin kotu, wanda ya nuna yiwuwar kalubale na shari’a nan gaba idan INEC ta ci gaba da jinkirin rajista.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp