Fiye Da Falasdinawa 90 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
Published: 8th, June 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza sun ambaci cewa a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 91. Mafi yawancin shahidan dai sun kwanta dama ne sanadiyyar hare-haren da sojojin HKI su ka kai musu a wuraren da aka ware na raba kayan agaji da ‘Yan Sahayoniya da Amurkawa suke tafiyar da su.
Bugu da kari, sojojin Amurka da suke a mashigar “Natasrim” sun ce; sun yi amfani da hayakin mai burkono akan fararen hulan Falasdinawa da suke gogoriyon samun abinci.
A yammacin Rafaha dake kudancin Gaza, Falasdinawa 4 ne su ka yi shahada a wurin raba kayan agaji yayin da wasu 70 su ka jikkata.
Tashar talabijin din ‘almaydin’ ta bayar da labarin dake cewa; Wani Bafalasdine guda daya ya yi shahada sanadiyyar bude masa wuta da sojojin mamaya su ka yi a mashigar “Natsrim” a yayin da yake kokarin isa inda zai sami abinci.
Shaidun ganin ido sun ce sojojin Amurka da suke a cikin wurin raba kayan agajin dake kudancin ” Natsarim” sun yi amfani da hayaki mai borkono akan fararen hula, da hakan ya sa da dama daga cikinsu su ka shake. An dauki da dama daga cikinsu zuwa asibitocin “Shuhada’ul-Aqsa’ da kuma “Audah” dake sansanin ‘yan hijira na Nusairat.
Dama dai kungiyar Hamas ta bayyana cewa; cibiyoyin raba kayan agaji da HKI da Amurka suke tafiyar da shi, ya zama wani tarko ne na kashe Falasdinawa. Kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD sun ki amincewa da su yi aiki a karkashin Amurka da HKI wajen raba kayan agajin saboda sun ce, yana da manufa ta soja da kuma korar Falasdinawa daga gidajensu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da Falasdinu a matsayin Mamba
Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba.
Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.
Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba.
“Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai wadanda ba su dace da manufofin Amurka ba,” in ji Kelly.
Ta ci gaba da cewa, shigar da Falasdinu a matsayin mamba a hukumar UNESCO, Amurka na Kallon hakan a matsayin babbar matsala kuma ya saba wa manufofin Amurka, wanda hakan ke ke kara haifar da karuwar kalaman kyama ga Isra’ila a cikin kungiyar.
Darakta-janar na UNESCO, Audrey Azoulay, ya bayyana matukar Rashin jin dadinsa kan matakin da Trump ya dauka na ficewa daga kungiyar, amma ya kara da cewa dama tuni aka yi hasashen haka, kuma UNESCO ta shirya ma hakan, tare da yin nuni da cewa hukumar ta dauki matakin karkata hanyoyin samar da kudadenta, inda kusan kashi 8% na kasafin kudin ta ke fiowa daga Washington.