Fiye Da Falasdinawa 90 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
Published: 8th, June 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza sun ambaci cewa a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 91. Mafi yawancin shahidan dai sun kwanta dama ne sanadiyyar hare-haren da sojojin HKI su ka kai musu a wuraren da aka ware na raba kayan agaji da ‘Yan Sahayoniya da Amurkawa suke tafiyar da su.
Bugu da kari, sojojin Amurka da suke a mashigar “Natasrim” sun ce; sun yi amfani da hayakin mai burkono akan fararen hulan Falasdinawa da suke gogoriyon samun abinci.
A yammacin Rafaha dake kudancin Gaza, Falasdinawa 4 ne su ka yi shahada a wurin raba kayan agaji yayin da wasu 70 su ka jikkata.
Tashar talabijin din ‘almaydin’ ta bayar da labarin dake cewa; Wani Bafalasdine guda daya ya yi shahada sanadiyyar bude masa wuta da sojojin mamaya su ka yi a mashigar “Natsrim” a yayin da yake kokarin isa inda zai sami abinci.
Shaidun ganin ido sun ce sojojin Amurka da suke a cikin wurin raba kayan agajin dake kudancin ” Natsarim” sun yi amfani da hayaki mai borkono akan fararen hula, da hakan ya sa da dama daga cikinsu su ka shake. An dauki da dama daga cikinsu zuwa asibitocin “Shuhada’ul-Aqsa’ da kuma “Audah” dake sansanin ‘yan hijira na Nusairat.
Dama dai kungiyar Hamas ta bayyana cewa; cibiyoyin raba kayan agaji da HKI da Amurka suke tafiyar da shi, ya zama wani tarko ne na kashe Falasdinawa. Kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD sun ki amincewa da su yi aiki a karkashin Amurka da HKI wajen raba kayan agajin saboda sun ce, yana da manufa ta soja da kuma korar Falasdinawa daga gidajensu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno
A wani hari ta kasa da na sama, rundunar sojojin Operation Hadin Kai sun dakile wasu manyan hare-haren ta’addanci guda biyu a ranar Alhamis a Jihar Borno.
Dakarun sun kashe da dama daga cikin maharan tare da kwato tarin makamai da alburusai.
Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a SaudiyyaRahoton da hukumar tsaron sojan Najeriya suka fitar na nuna cewar, dakarun sojan rundunar ta OPHK an kaddamar da hare-haren ne a wasu wurare daban-daban na sojoji a Buratai da ke karamar hukumar Biu da kuma Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam.
An bayyana cikakkun bayanan hare-haren a cikin wata sanarwa da Mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji na hedikwatar Operation Hadin Kai, Kyaftin Reuben Kovangiya ya fitar ranar Alhamis, 5 ga Yuni, 2025.
Sanarwar ta ce, lamarin na farko ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis a garin Buratai, inda ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa inda dakarun suke daga wurare da dama.
“Sojojin, duk da haka, cikin hanzari sun yi artabu da ‘yan ta’addan da manyan bindigogi, yayin da dakarun sama da manya-manyan Jiragen yakin Tucano suka ba da tallafi ta sama ga sojojin.”
Kyaftin Kovangiya ya bayyana daga bayan an gano gawarwakin ‘yan Boko Haram dama, tare da tarin makamai da alburusai iri-iri.
Hakazalika, sojojin a Mallam Fatori sun dakile wani harin da ‘yan tada kayar bayan suka tunkaro inda suke daga bangarori daban-dabam.
Sanarwar ta kara da cewa, “Sojojin sun yi wa ‘yan Boko Haram mummunan barna lamarin da ya sa su tserewa cikin rudani.”
Bayan da ‘yan tada kayar bayan da suka ja da baya ya kai ga kashe mutane da dama, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.
Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a Mallam Fatori sun hada da: bindigogi kirar AK-47 da yawa, manyan bindigogi masu linzami (GPMGs), bindigogin roka (RPGs), da sauran kayan aikinsu na ta’addanci.