An Kaddamar Da Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka A London
Published: 10th, June 2025 GMT
A yau Litinin 9 ga wata ne memban hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, kana mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, da jami’an bangaren Amurka, suka halarci taron farko na tattauna batutuwan tattalin arziki da cinikayya na Sin da Amurka, wanda aka kaddamar a birnin London dake kasar Birtaniya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Gabanin Taron Jam’iyyar
Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, ya bayyana cewa Gwamnonin APC sun gudanar da wata muhimmiyar ganawa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadar gwamnati da ke Abuja.
Da yake zantawa da manema labarai na Fadar Shugaban Ƙasa bayan kammala taron, Gwamna Uzodimma ya bayyana ganawar da cewa “tattaunawa ce mai muhimmanci da Shugaban Ƙasa domin ƙarfafa jam’iyyar da kuma inganta ikon ta na samar da nagartaccen shugabanci ga ‘yan Najeriya”.
Ya ƙara da cewa, a matsayin su na gwamnoni, sun haɗu da Shugaban Ƙasa domin daidaita matsayin al’amuran jam’iyya da kuma muhimman abubuwan da suka shafi shugabanci.
Da aka tambaye shi ko ana sa ran yanke wasu manyan shawarwari ko takaddama a yayin Taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC da za a gudanar a gobe Alhamis, gwamnan ya ce, “Ba za mu iya cewa komai yanzu ba har sai mun isa wurin taron gobe.”
Ana sa ran taron na gobe Alhamis 24 ga watan Yulin 2025 zai tattauna kan muhimman batutuwa da suka shafi jam’iyyar da kuma tsara hanyoyin ci gaba da haɗin kai da inganci a harkokin ta.
Bello Wakili