Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah
Published: 7th, June 2025 GMT
Gobara ta tashi a otal ɗin Imaratus Sanan da ke birnin Makkah a ƙasar Saudiyya, inda sama da alhazan Najeriya 48 suka sauka yayin aikin Hajjin shekarar 2025.
Otal ɗin yana unguwar Sharamansur a birnin Makkah.
Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da dukaHukumar Jin Daɗin Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta tabbatar da cewa dukkanin alhazan sun tsira kuma babu wanda ya ji rauni.
A cewar NAHCON, hukumomin gaggawa na Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin sun gaggauta kashe wutar kafin ta bazu.
Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman, ya ziyarci otal ɗin tare da wasu jami’an hukumar domin duba halin da ake ciki.
Ya bayar da umarnin a kwashe alhazan zuwa wani sabon otal cikin gaggawa, sannan ya yi alƙawarin tallafa musu.
“Muna gode wa Allah da babu rai da ya salwanta,” in ji shi.
Ya ce NAHCON za ta yi aiki da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa mahajjatan sun samu kulawa ta musamman.
“An riga an duba sabon wajen da za a sauke su, kuma an fara shirye-shiryen sauya wajen. NAHCON ta kuma yaba da saurin kai taimako da hukumomin Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin suka yi.”
Wasu daga cikin mahajjatan sun shaida wa Aminiya cewa gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Asabar, a lokacin da mafi yawan su ke Mina wajen gudanar da jifar shaiɗan, ɗaya daga cikin manyan ayyukan aikin Hajji.
NAHCON ta ce za ta ci gaba da sanar da al’umma yayin da ake ciki da zarar ta samu sabbin bayanai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Najeriya Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Domin shawo kan wannan matsalar, ministan ya zayyana kokarin da ake yi a karkashin dabarun bunkasa kiwon dabbobi na kasa, wanda ya mayar da hankali kan ginshikai guda 10 da suka hada da bunkasa kimar dabbobi, inganta kiwo, kiwon lafiyar dabbobi, samar da kudi, sauya salon kiwo da karfafawa matasa da mata gwiwa kan dogaro da kai.
Maiha ya yi tunin cewa zuwa yanzu ma’aikatar ta samu cimma wasu nasarori da suka hada da yin rajistar nau’in kiwo guda takwas, “na farko a cikin shekaru 48” da kuma samar da wani shiri na kasa kan albarkatun halittun dabbobi tare da hadin gwiwar FAO.
“Dabbobinmu na cikin gida suna samar da lita 1-2 na madara a kullun, idan aka kwatanta da na waje a karkashin gudanarwa da kuma tsarin kiwon lafiya domin shawo kan wanan gibin, dole ne mu tashi tsaye mu magance wannan matsalar,” ya shaida.
Ministan ya kuma bayyana yadda ake zuba jari a fannin kiwon lafiyar dabbobi, gami da fadada samar da alluran rigakafin a Cibiyar Nazarin Dabbobi ta Kasa (NBRI) daga allurai miliyan 120 zuwa miliyan 850 a duk shekara. An kuma kaddamar da wani wurin ajiyar alluran rigakafi mai amfani da hasken rana mai karfin awo miliyan 40 a Sheda da ke Abuja da dai sauran nasarori.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp