Aminiya:
2025-09-17@23:28:55 GMT

Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah

Published: 7th, June 2025 GMT

Gobara ta tashi a otal ɗin Imaratus Sanan da ke birnin Makkah a ƙasar Saudiyya, inda sama da alhazan Najeriya 48 suka sauka yayin aikin Hajjin shekarar 2025.

Otal ɗin yana unguwar Sharamansur a birnin Makkah.

Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta tabbatar da cewa dukkanin alhazan sun tsira kuma babu wanda ya ji rauni.

A cewar NAHCON, hukumomin gaggawa na Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin sun gaggauta kashe wutar kafin ta bazu.

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman, ya ziyarci otal ɗin tare da wasu jami’an hukumar domin duba halin da ake ciki.

Ya bayar da umarnin a kwashe alhazan zuwa wani sabon otal cikin gaggawa, sannan ya yi alƙawarin tallafa musu.

“Muna gode wa Allah da babu rai da ya salwanta,” in ji shi.

Ya ce NAHCON za ta yi aiki da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa mahajjatan sun samu kulawa ta musamman.

“An riga an duba sabon wajen da za a sauke su, kuma an fara shirye-shiryen sauya wajen. NAHCON ta kuma yaba da saurin kai taimako da hukumomin Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin suka yi.”

Wasu daga cikin mahajjatan sun shaida wa Aminiya cewa gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Asabar, a lokacin da mafi yawan su ke Mina wajen gudanar da jifar shaiɗan, ɗaya daga cikin manyan ayyukan aikin Hajji.

NAHCON ta ce za ta ci gaba da sanar da al’umma yayin da ake ciki da zarar ta samu sabbin bayanai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Najeriya Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa