HausaTv:
2025-07-23@23:49:22 GMT

Hamas Ta bayyana Cewa Kungiyar Zata Ci Gaba Da Yakin Har Zuwa Karshen Mamaya

Published: 7th, June 2025 GMT

Abu Ubaida kakakn dakarun Ezzuddeen Al-Qassam reshen soje na kungiyar Hamasa ya bayyana cewa dakarunsa zasu ci gaba da Yakar sojojin yahudawa har zuwa korarsu daga yankin zirin Gaza.

Abu Ubaida ya kara nda cewa, dakarun Hamas suna a madaka ga sojojin HKI babu jada baya babu janyewa daga matsayinsu.

Kafin haka dai a jiya Jumma’a dakarun na Hamas tare da hadin guiwa da na Saraya Qudus sun aiwatar da wani shiri ko tarko kan sojojin yahudawan wanda ya sami nasara halaka sojojin yahudawa da dam.

Majiyar yahudawan sun tabbatar da aukuwar hare-haren na Khan Yunus dake kudancin Gaza, wanda kuma ya halaka yahufawa da dama.,

Abu ubaida ya kammala da cewa aikin soje da suka yi a Khan Yunus da Jabali yak aiga halakar sojojin yahudawa 5 da kuma jikatar wasu. Ya ce sojojin Hamas sun sake farkawa don haka a jiya Jumma’a suka aikata ayukan soje masu yawa a gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”

Ofishin Fira ministan kasar Iraki ya fitar da bayani a yau Laraba akan abinda ya gudana a tsakanin Muhammad Shiya al-Sudani da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio a tattaunawar wayar tarho.

Sakataren harkokin wajen Marco Rubio ne ya kira yi fira ministan Iraki inda su ka tattauna alakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma halin da ake ciki a wannan yankin.

Sudani ya yi ishara da hare-haren bayan nan da aka kai wa cibiyoyin man fetur dake yankin Kurdistan na Iraki da kuma yankin Salahuddin a Karkuk.

Haka nan kuma ya ce a halin yanzu jami’an tsaro suna gudanar da bincike domin gano wadanda su ka kai harin.”

Haka nan kuma Fira ministan na kasar Iraki ya bayyana mamakinsa akan yadda kai harin ya faru a lokacin da aka kulla yarjejeniya a tsakanin ma’aikatar man fetur din Iraki da kuma kamfanoni masu zuba hannun jari daga Amurka.”

Fira ministan harkokin wajen na Iraki ya kuma yi Magana akan rundunar sa kai ta “Hashdus-sha’abi” yana mai cewa; ana yi wa dokokin tsaron Iraki kwaskwarima ne a gaban majalisar da zai shafi rundunar sa-kai din wacce cibiya ce da Iraki ta amince da ita a gwamnatance.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi