Leadership News Hausa:
2025-07-25@12:37:59 GMT

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

Published: 10th, June 2025 GMT

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

Mataimakin firaministan Sin He Lifeng, ya gana da babbar ministar kudin Birtaniya Rachel Reeves jiya Lahadi a birnin Landan, inda suka zurfafa musaya game da batutuwan da suka shafi tattalin arziki da hadin gwiwa a fannin hada-hadar kudade, da sauran batutuwan dake janyo hankulan kasashensu.

He, wanda kuma shi ne ya jagoranci tawagar kasar Sin a tattaunawar tattalin arziki da harkokin cinikayya tsakanin Sin da Birtaniya, ya ce kamata ya yi kasashen biyu su yi aiki tare, wajen aiwatar da muhimman kudurori da shugabannin kasashen suka cimma, su kuma ingiza nasarar dandalin tattalin arziki da cinikayya na Sin da Birtaniya, da zurfafa musaya da hadin gwiwa a dukkanin sassan tattalin arziki da cinikayyarsu, da ingiza cimma moriya tare, da wanzar da nasarori, da ci gaba da daidaita bunkasar alakarsu ta fuskar raya tattalin arziki.

A nata bangare kuwa, Reeves wadda ta jagoranci tawagar Birtaniya a tattaunawar, cewa ta yi bangaren kasarta na dora muhimmancin gaske ga hadin gwiwa da Sin, kuma a shirye yake ya karfafa tattaunawa, don aiwatar da sakamakon tattaunawar tattalin arziki da harkokin cinikayya tsakanin Birtaniya da Sin, da shigar da sabon kuzari ga hadin gwiwar tattalin arzikin sassan biyu. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arziki da

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce taron koli na Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU karo na 25 dake tafe, zai taimaka wajen bunkasa tattaunawa bisa matsayin koli, da zurfafa shawarwari, da hadin gwiwa tsakanin sassan biyu, lamarin da zai biya bukatu da moriyarsu, da ma na sauran sassan duniya baki daya.

Guo Jiakun, ya jaddada muhimmancin taron, kasancewar ya zo a gabar da harkokin cudanyar kasa da kasa ke fuskantar yanayi na tangal-tangal, da ma karuwar daukar matakan kashin kai daga bangare guda, da kariyar cinikayya.

Ya ce, hadin gwiwar sassan biyu, ya haifar da manyan nasarori a baya, wanda hakan ya bunkasa ci gaba da daukakarsu, tare da samar da tarin alfanu ga jama’arsu da yawanta ya kai biliyan biyu, kana ya samar da babbar gudummawa ga raya zaman lafiya, da ci gaban duniya baki daya. Kazalika, hadin gwiwar sassan biyu ya zamo misali na hadin gwiwar cimma moriyar juna, a sabon zamani na dunkulewar tattalin arzikin duniya.

Daga nan sai ya bayyana aniyar kasar Sin ta yin aiki tare da EU, wajen cimma nasarar taron, matakin da zai aike da kyakkyawan sako ga duniya, game da aniyarsu ta hada karfi da karfe, wajen kafa hadin gwiwa mai karfin gaske, da daga martabar cudanyar mabambantan sassa, da bude kofa da aiwatar da hadin gwiwa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
  • Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba
  • Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin
  • Jihar Kano Za Ta Hada Gwiwa FMBN Don Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Gabanin Taron Jam’iyyar
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu