Iran Ta Sami Nasara Akan Korea Ta Arewa Akarkashin Share Fagen Shiga Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon
Published: 11th, June 2025 GMT
Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta sami nasarar akan abokiyar karawarta ta kasar Korea Ta Arewa da kwallaye uku masu kyau a wasan da aka yi a filin wasa na “Azadi” na Tehran.
Kasashen biyu dai suna a karkashin; bangare na uku a Asiya saboda share fagen kai wa ga shiga gasar cin kofin kwallon duniya na 2026.
Dan wasa mai suna Muhammad Muhibbi ne ya ci kwallon farko, a mintuna 74 da fara wasan, sai kuma Mahdi Darimi a mintuna 77, sa Amir Husain Husain zadeh, a minti 3 da aka kara, bayan cikar mituna 90.
A bangaren kungiyar kwallon kafa ta Korea Ta Arewa kuwa, ta kammala wasannin nata da ‘yan wasa 10 bayan da aka kori daya daga cikinsu saboda adaidai mintuna na 66 daga fara wasa.
Sauran kungiyoyin da suke cikin wannan bangare na uku, da kuma su ka yi wasa a wannan rana, sun hada Uzbakistan da ta ci Qatar 3-0 a birnin Tashqand. Ita kuwa Kyrkizistan ta yi daya da daya da Hadaddiyar Daular Larabawa.
Iran ce a gaba a cikin bangaren nasu na uku; da take da maki 23, sai kuma Uzbakistan mai binta da maki 21, ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa tana da maki 15, yayin da Qatar take da maki 13. Kasar Kyrkizitan tana da maki 8, sai kuma Korea Ta Arewa mai maki 3.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Korea Ta Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Yayin da gasar wasannin kasa da kasa ta shekarar 2025 ke karatowa, an gudanar da bikin karba, da kaddamar da fitilar gasar a Asabar din nan, a shahararren gidan adana kayan tarihi na Sanxingdui, dake birnin Chengdu na kasar Sin.
Kaddamar da fitilar gasar a yau, ya alamta fara kidayar kwanaki 12, gabanin bude gasar karo na 12, wadda za ta gudana tsakanin ranakun 7 zuwa 17 ga watan Agusta dake tafe. An tsara kewayawa da fitilar tsawon kilomita 11, a yankunan biranen Chengdu, da Deyang, da Meishan, kuma mutane 120 za su yi karba-karbar kewayawa da ita, wanda hakan ke alamta ruhin gasar da kyakkyawan zumuncin da take kullawa.
An ayyana ‘yar wasan motsa jiki Huang Zhangjiayang daga birnin Chengdu, wadda ta taimakawa kasar Sin lashe lambar zinari a wasan nuna fasahohin lankwasa jiki yayin gasar Olympics ta lokacin zafi a birnin Paris, a shekarar bara, a matsayin wadda za ta fara zagayawa da fitilar. Yayin da kwararren dan wasan kwallon tebur na kasar Sin Ma Long, zai kasance na karshe da zai kewaya da fitilar. An baiwa Ma Long wannan dama ne bisa kwarewarsa, da kuma nasarori masu yawa da ya cimma, a gasannin da ya wakilci kasar Sin a cikinsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp