Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta sami nasarar akan abokiyar karawarta ta kasar Korea Ta Arewa da kwallaye uku masu kyau a wasan da aka yi a filin wasa na “Azadi” na Tehran.

Kasashen biyu dai suna a karkashin; bangare na uku  a Asiya saboda share fagen kai wa ga shiga gasar cin kofin kwallon duniya na 2026.

Dan wasa mai suna Muhammad Muhibbi ne ya ci kwallon farko, a mintuna 74 da fara wasan, sai kuma Mahdi Darimi a mintuna 77, sa Amir Husain Husain zadeh, a minti 3 da aka kara, bayan cikar mituna 90.

A bangaren kungiyar kwallon kafa ta Korea Ta Arewa kuwa, ta kammala wasannin nata da ‘yan wasa 10 bayan da aka kori  daya daga cikinsu saboda adaidai mintuna na 66 daga fara wasa.

Sauran kungiyoyin da suke cikin wannan bangare na uku, da kuma su ka yi wasa a wannan rana, sun hada Uzbakistan da ta ci Qatar 3-0 a birnin Tashqand. Ita kuwa Kyrkizistan ta yi daya da daya da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran ce a gaba a cikin bangaren nasu na uku; da take da maki 23, sai kuma  Uzbakistan mai binta da maki 21, ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa tana da maki 15, yayin da Qatar take da maki 13. Kasar Kyrkizitan tana da maki 8, sai kuma Korea Ta Arewa mai maki 3.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Korea Ta Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

A wannan lokaci da wasu sassa ke kafa shingaye, GCI na gina gadoji. Manufar na kuma karfafa gwiwar tattaunawa, da gudanar da shawarwari tsakanin sassan duniya masu bambance-bambance, ta yadda za a kafa managarcin tsarin hadin kan bil’adama mai dorewa. GCI da ranar tattaunawa tsakanin wayewar kan kasa da kasa ta MDD, za su kara zamewa duniya muhimman manufofi na “tafiya tare a tsira tare”!(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
  • Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
  • Rasha Tana Kokarin Kara Samun Gindin Zama A Cikin Nahiyar Afirka