Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha
Published: 10th, June 2025 GMT
Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Maryam Abacha ta musanta zarge-zargen da ake yi wa mijinta na wawure maƙudan kuɗaɗen ƙasar a lokacin da yake kan karagar mulki.
A wata hira da aka yi da ita a kafar talabijin ta TVC a yayin cika shekara 27 da rasuwar Abacha, Maryam ta nanata cewa bai sace kuɗaɗen Nijeriya, tana mai cewa, da gangan aka sauya manufarsa ta adana dukiyar ƙasar a ƙetare.
Maryam Abacha ta ƙalubalanci waɗanda ke zargin mijinta da wawure dukiyar talakawa da su gabatar da gamsasshiyar hujja kan zarge-zargensu, tana mai ɗiga ayar tambaya kan wane ne shaida kan kuɗaɗen da aka adana su?
“Shin ka ga sanya hannu ko wata hujja kan dukiyar da aka adana? Kuɗin da mijina ya ɓoye saboda amfanin ’yan Najeriya, sun yi batar-dabo cikin ’yan watanni. Mutane ba sa magana a kan wannan.”
Kazalika Maryam Abacha ta ce, “me ya sa ake caccakar mutum? Shin ana yin haka ne saboda ƙabilanci ko banbancin addini? Mece ce matsalar ’yan Najeriya?”
Maryam ta kuma caccaki ’yan Nijeriya kan yadda suka yi amanna da abubuwan da gwamnatocin bayan suka faɗa musu na cewa, sun karɓo kuɗaɗen da Abacha ya zuba su a asusun ƙasashen ƙetare.
Gwamnatocin Nijeriya daban-daban da aka yi, sun yi nasarar karɓo ɗaruruwan miliyoyin dala da aka adana su a asusun ƙasashen ƙetare bayan an ce Abacha ne ya sace su tare da ajiye a waje.
Ƙasashen da aka karɓo kuɗaɗen sun haɗa da Switzerland da Amurka da Birtaniya, inda aka yi amfani da su a wasu shirye-shiryen raya al’umma.
Marigayi Janar Sani Abacha ya jagoraci Nijeriya ne ƙarƙashin mulkin soji tsakanin 1993 zuwa 1998.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Kudin Nijeriya Maryam Abacha Maryam Abacha
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp