Aminiya:
2025-07-26@11:50:42 GMT

Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha

Published: 10th, June 2025 GMT

Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Maryam Abacha ta musanta zarge-zargen da ake yi wa mijinta na wawure maƙudan kuɗaɗen ƙasar a lokacin da yake kan karagar mulki.

A wata hira da aka yi da ita a kafar talabijin ta TVC a yayin cika shekara 27 da rasuwar Abacha, Maryam ta nanata cewa bai sace kuɗaɗen Nijeriya, tana mai cewa, da gangan aka sauya manufarsa ta adana dukiyar ƙasar a ƙetare.

Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe

 Maryam Abacha ta ƙalubalanci waɗanda ke zargin mijinta da wawure dukiyar talakawa da su gabatar da gamsasshiyar hujja kan zarge-zargensu, tana mai ɗiga ayar tambaya kan wane ne shaida kan kuɗaɗen da aka adana su?

“Shin ka ga sanya hannu ko wata hujja kan dukiyar da aka adana? Kuɗin da mijina ya ɓoye saboda amfanin ’yan Najeriya, sun yi batar-dabo cikin ’yan watanni. Mutane ba sa magana a kan wannan.”

Kazalika Maryam Abacha ta ce, “me ya sa ake caccakar mutum? Shin ana yin haka ne saboda ƙabilanci ko banbancin addini? Mece ce matsalar ’yan Najeriya?”

Maryam ta kuma caccaki ’yan Nijeriya kan yadda suka yi amanna da abubuwan da gwamnatocin bayan suka faɗa musu na cewa, sun karɓo kuɗaɗen da Abacha ya zuba su a asusun ƙasashen ƙetare.

Gwamnatocin Nijeriya daban-daban da aka yi, sun yi nasarar karɓo ɗaruruwan miliyoyin dala da aka adana su a asusun ƙasashen ƙetare bayan an ce Abacha ne ya sace su tare da ajiye a waje.

Ƙasashen da aka karɓo kuɗaɗen sun haɗa da Switzerland da Amurka da Birtaniya, inda aka yi amfani da su a wasu shirye-shiryen raya al’umma.

Marigayi Janar Sani Abacha ya jagoraci Nijeriya ne ƙarƙashin mulkin soji tsakanin 1993 zuwa 1998.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Kudin Nijeriya Maryam Abacha Maryam Abacha

এছাড়াও পড়ুন:

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Ya ce tituna a Arewa sun lalace kuma gwamnati tana nuna rashin kulawa ga yankin. “Jiya da jirgi zan biyo na taho, amma aka ɗage jirgi daga ƙarfe 3 na yamma zuwa 8 na dare, sai na taho ta mota. Daga Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano abin takaici ne. Wannan aikin titi tun lokacin farkon hawa gwamnatin APC ake yinsa.”

Kwankwaso ya kara da cewa ana gudanar da manyan ayyuka a Kudu cikin hanzari, amma an bar ayyuka masu mahimmanci a Arewa babu kulawa.

“Muna jin ana gina titi daga Kudu zuwa Gabas. Muna maraba da ci gaba a ko’ina a Nijeriya. Amma gwamnati tana ɗaukar duk arzikin ƙasa ta zuba a ɓangare ɗaya kaɗai, ba ta yin aiki da ra’ayin ‘yan ƙasa gaba ɗaya,” cewarKwankwaso.

Ya roƙi gwamnatin Tinubu da ta sake duba tsarin rabon arziki tare da tabbatar da yin adalci a dukkan yankuna.

“Lokaci ya yi da gwamnati za ta sauya, ta tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnati ce ta ƙasa gaba ɗaya, ba ta wani ɓangare kawai ba,” in ji Kwankwaso.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  • Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
  • Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
  • Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
  • Tinubu ya fi mayar da hankali wajen gina Kudancin Nijeriya — Kwankwaso
  • Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
  • Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare
  • WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya