Aminiya:
2025-11-16@20:48:29 GMT

Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha

Published: 10th, June 2025 GMT

Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Maryam Abacha ta musanta zarge-zargen da ake yi wa mijinta na wawure maƙudan kuɗaɗen ƙasar a lokacin da yake kan karagar mulki.

A wata hira da aka yi da ita a kafar talabijin ta TVC a yayin cika shekara 27 da rasuwar Abacha, Maryam ta nanata cewa bai sace kuɗaɗen Nijeriya, tana mai cewa, da gangan aka sauya manufarsa ta adana dukiyar ƙasar a ƙetare.

Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe

 Maryam Abacha ta ƙalubalanci waɗanda ke zargin mijinta da wawure dukiyar talakawa da su gabatar da gamsasshiyar hujja kan zarge-zargensu, tana mai ɗiga ayar tambaya kan wane ne shaida kan kuɗaɗen da aka adana su?

“Shin ka ga sanya hannu ko wata hujja kan dukiyar da aka adana? Kuɗin da mijina ya ɓoye saboda amfanin ’yan Najeriya, sun yi batar-dabo cikin ’yan watanni. Mutane ba sa magana a kan wannan.”

Kazalika Maryam Abacha ta ce, “me ya sa ake caccakar mutum? Shin ana yin haka ne saboda ƙabilanci ko banbancin addini? Mece ce matsalar ’yan Najeriya?”

Maryam ta kuma caccaki ’yan Nijeriya kan yadda suka yi amanna da abubuwan da gwamnatocin bayan suka faɗa musu na cewa, sun karɓo kuɗaɗen da Abacha ya zuba su a asusun ƙasashen ƙetare.

Gwamnatocin Nijeriya daban-daban da aka yi, sun yi nasarar karɓo ɗaruruwan miliyoyin dala da aka adana su a asusun ƙasashen ƙetare bayan an ce Abacha ne ya sace su tare da ajiye a waje.

Ƙasashen da aka karɓo kuɗaɗen sun haɗa da Switzerland da Amurka da Birtaniya, inda aka yi amfani da su a wasu shirye-shiryen raya al’umma.

Marigayi Janar Sani Abacha ya jagoraci Nijeriya ne ƙarƙashin mulkin soji tsakanin 1993 zuwa 1998.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Kudin Nijeriya Maryam Abacha Maryam Abacha

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Haka zalika, a 2025, an samu kararraki 28 na ‘yan Nijeriya da suka kashe kansu. Shari’ar ta shafi mutane daga kowane jinsi da kuma masu matsayi daban-daban, ciki har da dalibai da kuma ‘yan kasuwa.

Da yake zantawa wani dan jarida, masanin ilimin halayyar Dan’adam, kuma kwararre a kan lafiyar kwakwalwa, Dakta Shuab Waidi ya ce; batun kisan kai a halin yanzu, na bukatar da kulawar gaggawa ga mahukuntan kasa.

Ya ce, “Kididdigar na nuna cewa, a kowane minti 33; ana asarar rai a Nijeriya sakamakon kashe kai, don haka, akwai bukatar cikin gaggawa a bude tattaunawa game da kashe kai ta hanyar gwajin lafiyar kwakwalwa.

“Cutar tabin hankali, wani bangare ne na kisan kai da kai, amma kashe kai ba cutar tabin hankali ba ce, domin kuwa tana da alaka da yanayin dabi’a mai rikitarwa da kuma yanayin zamantakewa.

“A yayin da sama da mutum 720,000 ke mutuwa a duk shekara daga masu kashe kansu a duk duniya, Nijeriya ba za ta iya daukar wannan batu a matsayin gazawar dabi’a ko kuma sakamakon shan muggan kwayoyi kawai ba.

Har ila yau, shugaban sashen kula da masu tabin hankali na cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Keffi a Jihar Nasarawa, Dakta Hassan Galadima ya ce; yanayin kashe kai a halin yanzu, na nuna matukar halin damuwa da ake ciki.

“An fi samun maza fiye da mata wajen yunkurin kisan kai, ta yadda suka mayar da al’amarin tamkar wata gasa. Har ila yau, ana samun yukurin afkawa cikin teku, wanda a halin yanzu ya zama ruwan dare fiye da rataye kai ko shiga gaban motoci,” in ji shi.

Ya kuma alakanta hakan da abubuwa da dama da suka hada da matsin lamba na ilimi, tabarbarewar arziki da ramuwar gayya da asiri da sauran makamantansu da suka zama ruwan dare a tsakanin matasa.

Dalilan Da Ke Haifar Da Matsalar Kisan Kai

A nasa ra’ayin, Shugaban Kungiyar Likitocin Iyali na Nijeriya (SOFPON), shiyyar Kudu-maso-Kudu, Dakta Iyang Aniete ya ce; Nijeriya na fuskantar matsalar kunar-bakin-wake da ta barke, aka kuma yi shiru, ba a magana a kai.

Ya kara da cewa, “Tare da kiyasin mutuwar mutane 15,000 a duk shekara da kuma aikata laifin yunkurin kashe kai a kasar, inda kuma ake hana mutanen da ke cikin wahala neman taimako.

Kashi 77 cikin 100 na kashe-kashen da ake yi, na faruwa ne a kasashe na masu karamin karfi da matsakaita, Nijeriya mai yawan al’umma sama da miliyan 200, na daya daga cikin wuraren da ake samun masu kashe kawunansu a duniya, inda aka kiyasta masu kashe kansu da kashi 17.3 cikin 100,000, wanda ya zarce na duniya (10.5 cikin 100,000) da kuma Afirka (10.00) da kuma Afirka (10.00).

Ya ci gaba da cewa, yawan kunar bakin wake a Nijeriya ya zarce 10.5/100, 000 a duniya, sai kuma na Afirka 12.0/100,000, yayin da Lesotho ke kan gaba a 72.4/100,000. A shekarar 2023, an samu rahoton kashe mutane kusan 83 a Jihar Legas kadai.

Kashi 15 cikin 100 na wadanda suke kashe kansu, mutanen da ba a kula da su ne.”

A cewarsa, a wani bincike da aka gudanar a Nijeriya, kashi 80.6 cikin 100 na wadanda abin ya shafa maza ne, kashi 51.8 cikin 100 sun yi aure, kashi 33.6 cikin 100 dalibai ne, kashi 2.3 cikin 100 kuma suna tsakanin shekaru 25 zuwa 34.

“Mutuwar kashe kai, ana ganinta a matsayin wani babban zunubi, kuma haramun; wanda mugaye ne kadai ke iya yi, don haka; iyalan da abin ya shafa, galibi ana kyamar su tare da kin sakin jiki da su ta hanyar zamantakewa, don haka; sun gwammace su boye mutuwar ’yan’uwan nasu, domin kuwa suna bayyana irin wannan kisan kai a matsayin mutuwar ganganci.

“Yawancin shari’o’in da aka ruwaito, sun dogara ne da bayanan ‘yansanda da kuma na asibiti.

“Shaidar bincike kan halin kashe kai a Nijeriya sun hada da amfani da sinadarai, yanka kai, kona kai da kananzir, rataye kai da kuma amfani da bindigogi a matsayin hanyoyin kashe kai,” in ji shi.

A cewar wata mai ilimin sanin halayyar Dan’adam, Charity Dogo, “Daga cikin manyan abubuwan da ke jawo kashe kai, akwai abubuwa masu hadari na mutum, ciki har da matsalolin kudi, tarihin iyali na wani ya kashe kansa, rashin lafiya, rashin lafiyar jiki da shaye-shaye da sauran makamantansu.”

Ta kara da cewa, “Yayin da alakar da ke tsakanin kashe-kashe da tashe-tashen hankula, musamman bakin ciki da matsalar shan barasa ya samu wurin zama sosai a Nijeriya, yawancin kashe-kashen kuma na faruwa ne da gangan a lokutan rikici tare da rashin iya magance matsalolin rayuwa, kamar matsalolin kudi, rabuwar dangantaka ko ciwo mai tsanani da kuma rashin lafiya.

“Bugu da kari, fuskantar rikici, bala’o’i, tashin hankali, cin zarafi ko asara da kuma kebewa wuri guda na da alaka da wadannan kashe-kashe na kai, kai tsaye.”

Ta ci gaba da cewa, “Akwai alaka tsakanin yadda ake yada shafukan sada zumunta, ba tare da wata ka’ida ba; da kuma karuwar kashe-kashen da matasa ke yi.”

Charity ta kara da cewa, “Matsakaitan matasa a duniya a yau, suna kokawa game da matsalolin yau da kullum, wadanda ka iya taimakawa wajen fadawa wannan mummunan hali.

“Yanayin zama na yau da kullum, shi ma na taimakawa. Don haka, yawancinsu suna kokarin sarrafa shi tare da wuce gona da iri a kafofin watsa labaru, sannan muna da yawan cin zarafin juna a wadannan kafofi na watsa labaru.

“Wani abu da amfani da kafofin watsa labaru ke yi shi ne, yana bude wasu kofofi ko hanyoyi masu matukar cutarwa.”

Wata likitan mahaukata, Abimbola Owoeye, a nata ra’ayin, ta bayyana tabarbarewar zamantakewa a tsakanin iyalai a matsayin abin da ke matukar taimakawa.

Sannan ta lura cewa, yawancin matasa ba sa yin hulda tare da danginsu, suna zabar yin hulda ko abota da fasahar sadarwa (AI), a kan su yi alaka da dan’uwansu Dan’adam.

“Wannan rashin kyawawan dabi’u a tsakanin iyali da kuma hadin kai,” in ji ta, “na iya haifar da rashin matsaloli, musamman a kan lafiyar kwakwalwa.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola November 15, 2025 Rahotonni Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje November 15, 2025 Kotu Da Ɗansanda Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
  • Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
  • Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci