Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha
Published: 10th, June 2025 GMT
Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Maryam Abacha ta musanta zarge-zargen da ake yi wa mijinta na wawure maƙudan kuɗaɗen ƙasar a lokacin da yake kan karagar mulki.
A wata hira da aka yi da ita a kafar talabijin ta TVC a yayin cika shekara 27 da rasuwar Abacha, Maryam ta nanata cewa bai sace kuɗaɗen Nijeriya, tana mai cewa, da gangan aka sauya manufarsa ta adana dukiyar ƙasar a ƙetare.
Maryam Abacha ta ƙalubalanci waɗanda ke zargin mijinta da wawure dukiyar talakawa da su gabatar da gamsasshiyar hujja kan zarge-zargensu, tana mai ɗiga ayar tambaya kan wane ne shaida kan kuɗaɗen da aka adana su?
“Shin ka ga sanya hannu ko wata hujja kan dukiyar da aka adana? Kuɗin da mijina ya ɓoye saboda amfanin ’yan Najeriya, sun yi batar-dabo cikin ’yan watanni. Mutane ba sa magana a kan wannan.”
Kazalika Maryam Abacha ta ce, “me ya sa ake caccakar mutum? Shin ana yin haka ne saboda ƙabilanci ko banbancin addini? Mece ce matsalar ’yan Najeriya?”
Maryam ta kuma caccaki ’yan Nijeriya kan yadda suka yi amanna da abubuwan da gwamnatocin bayan suka faɗa musu na cewa, sun karɓo kuɗaɗen da Abacha ya zuba su a asusun ƙasashen ƙetare.
Gwamnatocin Nijeriya daban-daban da aka yi, sun yi nasarar karɓo ɗaruruwan miliyoyin dala da aka adana su a asusun ƙasashen ƙetare bayan an ce Abacha ne ya sace su tare da ajiye a waje.
Ƙasashen da aka karɓo kuɗaɗen sun haɗa da Switzerland da Amurka da Birtaniya, inda aka yi amfani da su a wasu shirye-shiryen raya al’umma.
Marigayi Janar Sani Abacha ya jagoraci Nijeriya ne ƙarƙashin mulkin soji tsakanin 1993 zuwa 1998.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Kudin Nijeriya Maryam Abacha Maryam Abacha
এছাড়াও পড়ুন:
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
“Ana kiransa da suna dokar binciken tntanet ta tsoratarwa, wadda kasashen da suka ci gaba da dama suka dade da yin watsi da ita. A karni na 21, ba za a iya tunanin cewa gwamnatin Nijeriya za ta tauye ‘yancin fadin albarkacin baki, wanda shi ne ginshikin mulkin dimokuradiyya.”
Atiku ya ce duk wata doka da ke take ‘yancin ‘yan kasa na yin tsokaci mai muhimmanci game da shugabanninsu ko a hanyoyin sadarwar zamani ko ta hanyar magana ba dimokuradiyya ba ce kuma kai tsaye take hakkokin Dan’adam ne.
“A cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata tun bayan da gwamnatin Tinubu ta fara daukan matakan da ke janyo kuncin tattalin arziki da yunwa da bakin ciki ga mutanen Nijeriya, mun shaida zanga-zanga da koke-koke daga ‘yan kasa da ba za su iya daukar mulkin rashin gaskiya ba. Duk da haka, maimakon sauraron ‘yan kasa sai gwamnatin ta zabi hanyar amfani da karfin hukumo da tsoratarwa wadda ta juya lamarin zuwa wani abu daban.
“Lallai abin bakin ciki ne na ganin ana take hakkin ‘yan kasa da kundin tsarin mulki ya tabbatar a lokacin da ya kamata dimokuradiyyarmu ta kasance mai bin tsari. Dole ne mu tunatar da gwamnatin Tinubu cewa babu gwamnati a lokacin da ta kasa kare ‘yancin ‘yan kasarta, komai karfinta kuwa. Yin haka abun ta da hankali ne kuma hakan yana nuna gazawar gwamnati a fili.”
Atiku ya ce tabbas gwamnati na da alhakin kula da doka da oda, babu ingantacciyar gwamnati da za ta harbi masu zanga-zangar lumana da harsashi mai rai ko ta boye a bayan dokoki tana musguna wa ‘yan kasa.
Ya ce rashin kulawar gwamnati Tinubu ga dokar kasa da kuma ci gaba da kin bin umarnin kotu sun zama shahararrun siffofinta mafiya suna a kasar nan a halin yanzu.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara da cewa tun farkon wannan gwamnati, kungiyar kare hakkin Dan’ada ta Amnesty ta soke wannan gwamnatin da take hakkin Dan’adam.
Ya ce haka ma wasu kungiyoyi masu muhimmanci kamar irinsu kungiyar ‘yan jaridu ta Nijeriya da kungiyar kare ajandar kafafen yada labarai sun yi korafi kan cin zarafin ‘yan jarida da ‘yan kasa ta hannun jami’an gwamnati.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA