Aminiya:
2025-11-02@06:25:13 GMT

An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato

Published: 11th, June 2025 GMT

Rayukan aƙalla mutum 15 sun salwanta a wasu sabbin hare-haren da aka kai  wasu ƙauyuka biyu na ƙaramar hukumar Mangu a Jihar Filato.

Shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala, ya shaida wa manema labarai cewa, a daren ranar Talata ce aka kashe mutum bakwai a kauyen Bwai sai kuma mutane takwas a kauyen Chinchim duk a ƙaramar hukumar ta Mangu.

Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya

Wannan lamari na daga cikin sabbin hare-hare da tashin hankali da ke ci gaba da faruwa a yankin a wannan makon tsakanin yan kabilar Mwaghavul da Fulani.

Hare-hare daban-daban guda uku da suka faru a yankin ƙaramar hukumar Mangu a ranar Litinin da Talata, sun biyo bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya da ake kyautata zaton sun fara ne yayin da mutane ke aikin haƙar ma’adinai a yankin da ke da arzikin Tin, a cewar shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala.

Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ta ruwaito Emmanuel Bala yana cewa, “Makiyayan Fulani Musulmai masu yawo da dabbobi sun daɗe suna samun saɓani da manoma da suke zaune a Jihar Filato — waɗanda mafi yawansu Kiristoci ne — kan rikicin mallakar fili da albarkatun ƙasa.”.

Ya ƙara da cewa hare-haren da ake kai wa a yankin sau da yawa na da nasaba da bambancin ƙabila da addini, wanda ke haifar da hare-haren ramuwar gayya marasa kakkautawa.

“Watanni da suka wuce, wasu mazauna yankin na aikin haƙar ma’adinai, sai aka kai musu hari da adduna, kodayake babu wanda ya mutu a harin farko.

“Amma bayan jerin ramuwar gayya da martani, an kai hare-hare uku a ranar Litinin da Talata, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 20,” in ji Bala.

Wani jami’in Red Cross ya tabbatar da adadin waɗanda suka mutu cikin sa’o’i 24 a harin Chinchin, yana mai cewa adadinsu na iya kai wa 21.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Jihar Filato ƙaramar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa, wata gobara ta ƙone wani shagon Adidas Sports da ke cikin rukunin babban kantin nan na sayar da kayayyaki na Jabi Lake Mall, Abuja da tsakar daren Alhamis.

Daily Trust ta ruwaito cewa, shagon ne kaɗai gobarar ta shafa.

An kuma samu rahoton cewa, an baza jami’an kashe gobara daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da na Kamfanin Berger da na hukumar kashe gobara ta Abuja da kuma jami’an ’yan sanda zuwa wurin.

Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29

A lokacin da Wakilin Daily Trust ya kai ziyara da safe zuwa wurin, an shawo kan gobarar.

Wani ma’aikaci a shagon ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce, ba a samu asarar rai ba a wurin. Ya kuma tabbatar da cewa, “Shagon sayar da kayan Wasannin Adidas ne kawai gobarar ta shafa.”

Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta babban birnin tarayya, Ibrahim Mohammad, ya tabbatarwa da majiyar da faruwar lamarin, amma ya ce ƙarama ce.

Ya ce, an shawo kan lamarin kuma an dawo da zaman lafiya.

Ita ma da take mayar da martani, kakakin rundunar ’yan sandan Birnin Tarayya, Josephine Adeh ta ce an tura jami’an ’yan sanda wurin da lamarin ya faru domin kare yankin da kuma hana sace-sacen jama’a.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:40 na asubahi, nan take muka tura mutanenmu wurin domin su tsare wurin da kuma hana duk wani abu da ya saɓa wa zaman lafiya,” in ji ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi
  • Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati