Birnin Los Angeles na Amurka tana ci gaba da fuskantar tashe-tashe hankula kamar yadda zanga-zanga ta mamaye birnin

An ayyana dokar ta-baci a birnin Los Angeles na Amurka yayin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin masu zanga-zanga da ‘yan sanda kan batun gwamnatin kasar kan batun neman murkushe bakin haure.

Gwamnan California Gavin Newsom ya zargi shugaba Donald Trump da rura wutar zanga-zangar.

Gavin Newsom ya dauki Trump a matsayin wani mai karya kundin tsarin mulki ta hanyar korar bakin haure da yawa ba tare da nuna bambanci ba, yana mai bayyana tura dakarun Marines da na National Guard a matsayin wani kara ruruta water tashin hankali na rashin hankali da zai kara tada zaune tsaye a birnin.

Bayan Donald Trump ya bayyana bakin haure a matsayin dabbobi da ke dauke da tutocin wasu kasashe, Trump ya yi alkawarin cewa ba zai kyale abin da ya kira ‘yan mamaya da bakin haure daga kasashe masu tasowa na duniya su mamaye birnin California ba kuma zai bankado masu ba da tallafi ga masu zanga-zangar a California.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata

Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan birnin Hudaidah na bakin ruwa a kasar Yemen a safiyar yau Talata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto tashoshin talabijin ta Almasirahtv ta kasar Yemen, da kuma Aljazeerah ta kasar Qatar  suna bada wannan labarin.

Sun kuma kara da cewa tun fara yaki a Gaza a shekara ta 2023 sojojin kasar Yemen suka hana jiragen kasuwanci na HKI wucewa ta babul Mandab na kasar Yemen wanda ya jawowa HKI asarori masu yawa, ya kuma gurgurta ayyukan tashoshin jiragen Ruwa na ummu Rashrash ko Ilat da kuma Haifa.

Sannan suna kaiwa hki hare-hare ne da makamai masu linzami kan tashar jiragen sama na Bengerion da kuma wuraren soje na kasar tun lokacin

Yemen na yin haka ne don goyon bayan  ga al-ummar Falasdinawa wadanda sojojin HKI suke ci gaba da yi masu kisan kare dangi tun lokaci har zuwa yanzu. Falasdinawa kimani 54000 hki ta kace ya zuwa yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  •  Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
  • Za’ayi tattaunawa ta gaba tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi a Oman
  • Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya
  • Trump: Yadda Sabuwar Dokar Hana Shiga Amurka Ta Fi Shafar Musulmai Da Afirka
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata