HausaTv:
2025-11-13@21:35:42 GMT

Iran Ta Sami Muhimman Bayanai Na Sirri Akan Shirin Nukiliyar HKI

Published: 8th, June 2025 GMT

Tashar talabijin din ‘almayadin” ta ambato wata majiya ta Iran tana cewa; Jami’an leken asirin kasar sun sami muhimman byanai akan Shirin Nukiliyar HKI.

Majiyar ta kara da cewa; Jami’an leken asirin Iran sun iya isa ga wadannan muhimman bayanan masu yawan gaske tare da yin jigilarsu zuwa cikin kasar Iran.

Daga cikin bayanan da akwai wadanda su ka shafi shirye-shiryen da ‘yan sahayoniyar suke aiwatarwa na Nukiliya da kuma cibiyoyin Nukiliyar.

Majiyar ta kara da cewa;  jami’an leken asirin na Iran sun iya kai wa ga wadannan bayanan tun shekarun  da su ka gabata, kuma saboda yawan bayanan da kuma hanyoyin shigo da su cikin Iran ne ya sa ba a bayyana shi ba sai yanzu.

Haka nan kuma majiyar ta ce bayanan sun hada hotuna na cibiyoyin Nukiliyar HKI da kuma bidiyo da suka bukaci lokaci mai tsawo na yin nazarinsu.

Majiyar almayadin ta ce; Abu ne mai yiyuwa mutanen da HKI ta bayyana cewa ta kama su a cikin kwanakin bayan nan, suna da alaka da wadannan bayanan da su ka shiga hannun Iran.

Har ila yau, tashar talabijin din ta kuma ambaci cewa; Fitar da wannan sanarwar a wannan lokacin yana da nashi muhimmanci bisa la’akari da halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama

A jiya Laraba ne aka bude shari’ar tsohon madugun ‘yan tawayen kasar DRC Roger Lombala a kasar Faransa bisa tuhumar da ake yi masa da aikata laifuka akan bil’adama a yayin yakin DRC na biyu. Ana kuma tsammanin cewa wannan shari’ar za ta dauki wata daya ana yinta.

A yayin zaman shari’ar za a gabatar da shaidu daga wadanda su ka cutu sanadiyyar ayyukan kungiyar ‘yan tawayen wacce Lombala ya jagoranta.

Wannan shi ne karon farko da za a yi wa dan kasar DRC shari’a a kasar Faransa bisa ka’idar hurumin shari’a na duniya.

Ofishin Fada Da Laifuka Aka Bil’adama ( OCLCH)  ya kama Lombala ne a ranar 29 ga watan Disamba 2020 a birnin Paris. An kuma gabatar da shi a gaban kotu a ranar 2 ga watan Janairu 2021 inda aka tuhume shi da; “Kitsa makirci da  zummar aikata manyan laifuka akan bil’adama” da kuma ” Makarkashiyar aikata laifuka akan bil’adama.”

 A cikin watan Nuwamba na 2023 aka tuhumi madugun ‘yan tawayen a karkashin wani tsari da doka da yake bai wa wata kasa yin shari’a akan laifuka masu hatsari da aka tafka, ba tare da la’akari da inda inda aka yi laifukan ba.

Ana zargin Lombala da  kungiyarsa da cewa ya aikata laufukan a tsakanin watan Oktoba na 2002 zuwa watan janairu na 2003 a karkashin kungiyarsa ta “Gamayyar ‘yan Demokradiyya da Masu Kishin Congo” wacce kasar Uganda take taimakawa. A wancan tsakanin kungiyar ta yi kokarin shimfida ikonta a yankin Bini wanda yake cike da ma’adanai a gundumar Itori ta gabas. Daga cikin laifukan nasu da akwai kisa da kuma fyade da wawason dukiyar al’umma.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji November 13, 2025   Janar Ali Fadwi: Muna Aiki Tukuru Domin Sabunta Nisan Makamanmu Masu Linzami November 13, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Iran da Rasha sun Tattauna Gabanin Taron Gwamnonin IAEA November 13, 2025 Iraki: An Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar November 13, 2025 Kenya: An gano tarin zinari a karkashin kasa da darajarsa ta haura Dala biliyan 5 November 13, 2025 Gaza: Hamas Ta Nemi Kawo Karshen Kisan Kiyashi Da Lamunce  Shigar Da Taimako November 13, 2025 MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya November 13, 2025 Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza November 12, 2025 Shugaban Iran Ya Aike Da Wasika Ta Musamman Zuwa Ga Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiyya November 12, 2025 Gwamntin Nijeriya tace Za ta Kare Sojojinta Da Ke Bakin Aiki November 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe
  • Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na  Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO)
  • Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
  • Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba
  • An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori