Iran Ta Sami Muhimman Bayanai Na Sirri Akan Shirin Nukiliyar HKI
Published: 8th, June 2025 GMT
Tashar talabijin din ‘almayadin” ta ambato wata majiya ta Iran tana cewa; Jami’an leken asirin kasar sun sami muhimman byanai akan Shirin Nukiliyar HKI.
Majiyar ta kara da cewa; Jami’an leken asirin Iran sun iya isa ga wadannan muhimman bayanan masu yawan gaske tare da yin jigilarsu zuwa cikin kasar Iran.
Majiyar ta kara da cewa; jami’an leken asirin na Iran sun iya kai wa ga wadannan bayanan tun shekarun da su ka gabata, kuma saboda yawan bayanan da kuma hanyoyin shigo da su cikin Iran ne ya sa ba a bayyana shi ba sai yanzu.
Haka nan kuma majiyar ta ce bayanan sun hada hotuna na cibiyoyin Nukiliyar HKI da kuma bidiyo da suka bukaci lokaci mai tsawo na yin nazarinsu.
Majiyar almayadin ta ce; Abu ne mai yiyuwa mutanen da HKI ta bayyana cewa ta kama su a cikin kwanakin bayan nan, suna da alaka da wadannan bayanan da su ka shiga hannun Iran.
Har ila yau, tashar talabijin din ta kuma ambaci cewa; Fitar da wannan sanarwar a wannan lokacin yana da nashi muhimmanci bisa la’akari da halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Yobe, sun fara rabon kayayyakin gini ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a ƙananan hukumomi 13 na jihar.
Wannan taimako na da nufin tallafa wa mutanen da ambaliya ta rushe musu gidaje.
Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido An kone babur din ‘barayin waya’ a KanoA lokacin da aka fara rabon kayayyakin a Damaturu, wakilin babban daraktan NEDC, Farfesa Ibrahim Ali Abbas, ya ce hukumar ta kawo kayayyakin rufin gida da sauran kayan gini don taimaka wa mutane su gyara ko sake gina gidajensu.
Baya ga wannan, hukumar ta kuma bai wa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), kayan aikin ceto, domin su kasance cikin shiri idan wani iftila’i ya sake faruwa a wannan daminar.
Babban jami’in na NEDC ya roƙi shugabanni da su raba kayan cikin gaskiya da adalci, kuma a tabbatar cewa kayan sun kai hannun masu buƙata yadda ya dace.
A nata ɓangaren, Kwamishiniyar Ma’aikatar Agaji da Jin-ƙai ta Jihar Yobe, Dokta Mairo Ahmed Amshi, ta yaba wa hukumar NEDC saboda taimakon a kan lokaci.
Ta ce wannan matakin zai rage wa mutanen da ambaliya ta shafa raɗaɗi da damuwa.
Ta kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa waɗanda abin ya shafa, da kayan abinci, magunguna da kuma sansanin zama na wucin gadi.
Amma ta buƙaci shugabannin al’umma da su kula da yadda ake raba kayan, sannan ta roƙi wadanda suka samu tallafin da su yi amfani da shi wajen gina gidajen da za su ba su kariya da kwanciyar hankali.