HausaTv:
2025-08-01@05:00:05 GMT

Majalisar Dattijan Aljeriya Ta Soke Duk Wata Hulda Da Majalisar Dattijan Faransa

Published: 27th, February 2025 GMT

Majalisar Dattijan Aljeriya ta “dakatar da duk wata hulda da Majalisar Dattijan Faransa.

Majalisar al’ummar kasar, kwatankwacin majalisar dattijai a kasar Aljeriya, ta sanar da cewa ta “dakatar da dangantakarta” da majalisar dattawan Faransa, domin nuna adawa da ziyarar da shugabanta Gérard Larcher ya kai a ranakun Litinin da Talata a yankin yammacin Sahara.

Ziyarar ta biyo bayan wani gagarumin sauyi da shugaba Emmanuel Macron ya yi a watan Yulin shekarar 2024, inda ya nuna goyan baya  ga shirin cin gashin kan yankin “karkashin ikon mulkin Moroko” wanda ya haifar da fushin Algiers.

Yankin da Spain ta yi wa mulkin mallaka na yammacin Sahara, wani yanki ne na hamada da Majalisar Dinkin Duniya ba ta yanke matsayi kansa ba, kashi 80% na kasar Maroko ne ke iko da shi, amma kungiyar ‘yan awaren Polisario, da ke samun goyon bayan Aljeriya, ta kwashe shekaru 50 tana fafatukar neman samun ‘yancinsa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattijan da Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa

Kwamitin neman sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba daga Karamar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa, ya gabatar da takardar bukatarsa ga kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da kirkiro jihohi da kananan hukumomi a zaman da aka yi a jihar Kano.

A yayin mika takardar, Shugaban kwamitin kuma Hakimin Kanya Babba,  Makaman Ringim, Malam Mohammed Ibrahim ya bayyana cewar wannan yunkuri ya bi duk sharuddan da kundin tsarin mulki ya shimfida don kafa sabuwar karamar hukuma.

 

Makaman na Ringim ya kara da cewar, daukacin al’ummar yankin Kanya Babba, ciki da wajen mazabar na matukar goyon bayan hakan domin bunkasa ci gaban tattalin arziki da al’umma a yankin.

Da yake karbar takardar, Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibril, ya nuna jin dadin sa da jajircewar mutanen Kanya Babba wajen mika takardar.

Barau Jibrin, ya kuma tabbatar musu kwamitinsa zai yi adalci da gaskiya a aikin da aka dora musa.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, taron mika bukatar ya samu halartar mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman da Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Alhaji Babangida Husaini da dan majalisar jiha mai wakiltar mazabar Kanya, Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu da mai bawa gwamna shawara kan harkokin bada aiyukan kwangila Usman Haladu Isa da Alhaji Salisu Muazu Kanya da hakimai da Dagatai da ‘yan siyasa da kuma sauran masu ruwa da tsaki da dimbin masoya.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran