Aminiya:
2025-09-18@02:21:33 GMT

Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu

Published: 11th, June 2025 GMT

Mahara sun kone gidaje akalla 96 a yankin Gyenbwas na gundumar Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Mazauna yankin sun kuma yi zargin cewa maharan sun kuma kwashe musu kayan abinci da katifu da kuma shanu da sauran kayayyaki.

Alhaji Yakubu Umar, wanda kuma shi ne Madugun Langai ne ya shaida wa Aminiya hakan a ranar Talata.

A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alau — Gwamnatin Borno Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara

Ya kuma ce bayan mutum biyun da aka kashe musu ranar Litinin, sun kuma kara samo gawar mutum daya a yankin, wanda hakan ya kai adadin mutanen da aka kashe yayin harin zuwa uku.

Mazauna yankin dai na zargin ’yan kabilar Birom da kai musu harin, kodayake su kuma sun musanta hakan.

A cewar Alhaji Yakubu, “Ba a taba yi mana irin wannan ta’addancin ba. maharan sun kone kayan amfani masu yawa ciki har da sutturu da kuma kayan abinci. Sannan sun sace kayayyakinmu na miliyoyin naira. Mu a gaskiya muna zaune da kowa lafiya a nan, shi ya sa ma harin ya yi matukar daure mana kai.

Daga nan sai ya yi kira da gwamnati da ta binciki harin domin ta hukunta wadanda ke da hannu a ciki sannan ta kai wa wadanda suka yi asara tallafi.

Ba mu muka kai harin ba – Birom

Sai dai Kungiyar Matasa Birom (BYM) ta karyata labarin kai harin, inda ta bayyana shi a matsayin na kanzon kurege.

Shugaban kungiyar, Dalyop Solomon, ya ce, “Jiya akwai mambobinmu uku da aka kai wa hari yayin da suke aiki a gonakinsu, wadanda yanzu haka suna asibiti ana kula da su. Abin da muka sani kawai shi ne mutanenmu na cikin fargaba, kawai Fulani na fitowa ne saboda su samu dalilin kai mana hari.

“Amma ya kamata su sani, duk lokacin da suka kai mana hari, muna da ’yancin kare kanmu. Ba mamaki abin da ya faru ke nan. An zo kawo musu hari suka fatattaki maharan har zuwa maboyarsu, amma mu ba mu taba kai wa Fulani wani hari ba,” in ji Dalyop.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari

এছাড়াও পড়ুন:

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

 

Har ila yau, Lin ya ce matsayin kasar Sin dangane da rikicin kasar Ukraine bai sauya ba, cewa tattaunawa, da gudanar da shawarwari ne kadai hanyoyi mafiya dacewa na warware rikicin. Har kullum Sin na kan turbar adalci game da rikicin, tana kuma ci gaba da ingiza bukatar komawa teburin shawara tun barkewar rikicin. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta.
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar