Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu
Published: 11th, June 2025 GMT
Mahara sun kone gidaje akalla 96 a yankin Gyenbwas na gundumar Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.
Mazauna yankin sun kuma yi zargin cewa maharan sun kuma kwashe musu kayan abinci da katifu da kuma shanu da sauran kayayyaki.
Alhaji Yakubu Umar, wanda kuma shi ne Madugun Langai ne ya shaida wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Ya kuma ce bayan mutum biyun da aka kashe musu ranar Litinin, sun kuma kara samo gawar mutum daya a yankin, wanda hakan ya kai adadin mutanen da aka kashe yayin harin zuwa uku.
Mazauna yankin dai na zargin ’yan kabilar Birom da kai musu harin, kodayake su kuma sun musanta hakan.
A cewar Alhaji Yakubu, “Ba a taba yi mana irin wannan ta’addancin ba. maharan sun kone kayan amfani masu yawa ciki har da sutturu da kuma kayan abinci. Sannan sun sace kayayyakinmu na miliyoyin naira. Mu a gaskiya muna zaune da kowa lafiya a nan, shi ya sa ma harin ya yi matukar daure mana kai.
Daga nan sai ya yi kira da gwamnati da ta binciki harin domin ta hukunta wadanda ke da hannu a ciki sannan ta kai wa wadanda suka yi asara tallafi.
Ba mu muka kai harin ba – Birom
Sai dai Kungiyar Matasa Birom (BYM) ta karyata labarin kai harin, inda ta bayyana shi a matsayin na kanzon kurege.
Shugaban kungiyar, Dalyop Solomon, ya ce, “Jiya akwai mambobinmu uku da aka kai wa hari yayin da suke aiki a gonakinsu, wadanda yanzu haka suna asibiti ana kula da su. Abin da muka sani kawai shi ne mutanenmu na cikin fargaba, kawai Fulani na fitowa ne saboda su samu dalilin kai mana hari.
“Amma ya kamata su sani, duk lokacin da suka kai mana hari, muna da ’yancin kare kanmu. Ba mamaki abin da ya faru ke nan. An zo kawo musu hari suka fatattaki maharan har zuwa maboyarsu, amma mu ba mu taba kai wa Fulani wani hari ba,” in ji Dalyop.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Sake Tunzura Iran Shirin Makamashin Nukiliyarta Zai Fuskanci Martani
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Sake kunna ‘hanyar tayar da hankali’ zai gamu da martani mai ƙarfi na Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Fitar da kudiri kan Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta yi ba zai shafi kudurin al’ummar Iran ba ko kuma ci gaban shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya.
A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Iran a yammacin ranar Talata, Baqa’i ya yi la’akari da dukkanin rahotanni da kudurorin da suka shafi siyasa. Ya kuma kara da cewa Iran ba ta keta hurumin da ya rataya a wuyanta ba, kuma kasashen yammacin turai suna dora barazanarsu ne kan zargin da aka shafe shekaru 20 ana yi. Ya jaddada cewa Iran ba za ta yi watsi da hakkinta na inganta sinadarin Uranium ba.
Ya yi nuni da cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, Rafa’el Grossi, yana aiki ne da son zuciya, da kuma maimaita labaran bangarorin da ke adawa da Iran, ya kara da cewa, mayar da “hanyar tayar da hankali” za ta fuskanci martani mai karfi na Iran.
Dangane da matsayin Sanya batun Iran a gaba a hukumar ta IAEA da kuma barazanar da kasashen Turai ke yi na fitar da wani kuduri a taron majalisar alkalan hukumar IAEA da ke gudana a halin yanzu, ya bayyana cewa, batun nukiliyar Iran wani kuduri ne na siyasa kawai tun da farko, a lokacin da ya shiga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kuma kafin nan, lokacin da ake kallon lamarin a matsayin wani lamari mai yaduwa.