Minitan kiwon lafiya na kasar Iran ya bukaci kamfanonin da suke kera kayalin kiwon lafiya da kuma aikin likita so kara yawan kayakin da ake sayarwa zuwa kasashen waje.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Mohammad Reza Zafarkhan yana wannan kiran a jawabin da ya gabatar a taron bude kasuwar baje koli na kayalin aikin likita da kuma kiwon lafiya a nan Tehran.

Ministan ya kara da ce wa duk tare da mummunan takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma musamman Amurka ta dorawa kasar wannan bai hana ta ci gaba a fannonin ilmi masu yaw aba. Wanda ya kaita kasa da wasu manya-manyan kasashen duniya a wasu fagagen.

Ministan ya bukaci kamfanonin kera kayakin likita da kiwon lafiya a kasar da su kyautata ayyukansu a kan kayakin da suke kerawa ta yadda su zasu sayar da kansu ba tare da an tallatasu ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyim Musulmi A Nan Iran Da Sauran kasashen Duniya Ne Suka Yi Sallar Idin Layyah

Miliyoyin musulmi a nan kasar Iran da kuma sauran kasashen duniya suka gudanar da sallar Layyah, wanda yake daga cikin manya-manya bukukuwa a cikin addinin musulunci.

Tashar talabijin na Press tv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan sallar wanda maniyya da kuma sauran musulni suke yi ya hada da yanka dabba gwagwadon hali, da kuma raba namansa a tsakanin mabukata musulmi. Don tunawa da annabi Ibrahim a lokacinda ya yi kokarin yanka dansa annabi Isma’ila duk da cewa shi kadai ne yake da shi. Kuma yana sonsa, da yayi haka sai All..T ya fance shi da rago, don haka a mai makon dansa ya yanka rago,

Ana son duk musulmi baligi wanda ya ke da lafiya da ikon zuwa Hajja to yayi shi akalla sau

Guda a rayuwarsa.

A Bana dai musulmi kimani 1600,000 suka sauke farali. Mafi yawa daga kasashen waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Kiwon Lafiya Na Iran Ya Bukaci A Yawaita Sayar Da Kayakin Likita Zuwa Kasashen Waje
  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran
  • Iran: Matakan Washington Na Hana ‘Yan Kasashen Musulmi Shiga  Amurka  Kiyayya Ce
  • Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
  • Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Miliyoyim Musulmi A Nan Iran Da Sauran kasashen Duniya Ne Suka Yi Sallar Idin Layyah