HausaTv:
2025-11-02@19:44:11 GMT

Kungiyar Bada Agaji Ta  ‘Red Cross” Ta Ce Ta Fice Daga Jumhuriyar Nijer

Published: 7th, June 2025 GMT

vvddxfKungiyar bada agaji ta  Red Cross ta nbada sanarwan cewa ta rufe ofishinta a Nijer kuma ta fidda dukkan ma’aikatanta na kasashen waje daga kasar.

Ta kuma kara da cewa, gwamnatin kasar ta bukacin kungiyar ta fice daga Nijer tun watanni 4 da suka gabata, amma bata yi hakan bas ai yanzu.

ICRC ta tabbatar da hakan a ranar Alhamis da ta gabata Sannan Patric Yousuf daraktan kungiyar a Nahiyar Afirka ya bayyana cewa sun janye ma’aikatansu a Nijer sannan suna tattaunawa da gwamnatin kasar don sake dawowa kasar da kuma ci gaba da ayyukansu na bada agaji.

A cikin watan Fabrayrun wannan shekara ne ministan harkokin wajen kasar ya bada wannan umrnin ba tare da bayyana dalilan yin haka ba.

Kungiyar ta bada sanarwan cewa tun watan Fabrairun wannan shekara ne suke bin jami’an gwamnatin sojojin kasar domm samun takamemmen dalilin da yaaa sa suka dauki wannan matakin amma daga karshe sun fice daga kasar bayan sojojin sun dage a kan rufe ofishin kungiyar

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Ofishin kula da zirga-zirgar kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin ya ce, an harba kumbon Shenzhou-21 mai dauke da ‘yan sama jannatin kasar Sin 3 cikin nasara, a daren jiya Juma’a, agogon Beijing.

Daga baya kumbon ya sarrafa kansa wajen hade jikinsa da na tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, ta yadda ‘yan saman jannatin suka shiga tashar, inda tsoffin ‘yan saman jannati 3 da suka dade a cikin tashar, suka yi musu maraba. Hakan ya shaida haduwar sabbi da tsoffin ‘yan sama jannatin kasar Sin karo na 7 a tashar binciken sararin samaniya ta kasar.

Bisa shirin da aka yi, wadannan ‘yan sama jannati 6 za su kwashe kimanin kwanaki 5 suna aiki tare a cikin tashar, kafin tsoffin ‘yan saman jannatin 3 su kama hanyar dawowa gida.

Zuwa yanzu, kasar Sin ta riga ta tura ‘yan sama jannati 44 zuwa sararin samaniya. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung  November 1, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik November 1, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa