Kungiyar Bada Agaji Ta ‘Red Cross” Ta Ce Ta Fice Daga Jumhuriyar Nijer
Published: 7th, June 2025 GMT
vvddxfKungiyar bada agaji ta Red Cross ta nbada sanarwan cewa ta rufe ofishinta a Nijer kuma ta fidda dukkan ma’aikatanta na kasashen waje daga kasar.
Ta kuma kara da cewa, gwamnatin kasar ta bukacin kungiyar ta fice daga Nijer tun watanni 4 da suka gabata, amma bata yi hakan bas ai yanzu.
ICRC ta tabbatar da hakan a ranar Alhamis da ta gabata Sannan Patric Yousuf daraktan kungiyar a Nahiyar Afirka ya bayyana cewa sun janye ma’aikatansu a Nijer sannan suna tattaunawa da gwamnatin kasar don sake dawowa kasar da kuma ci gaba da ayyukansu na bada agaji.
A cikin watan Fabrayrun wannan shekara ne ministan harkokin wajen kasar ya bada wannan umrnin ba tare da bayyana dalilan yin haka ba.
Kungiyar ta bada sanarwan cewa tun watan Fabrairun wannan shekara ne suke bin jami’an gwamnatin sojojin kasar domm samun takamemmen dalilin da yaaa sa suka dauki wannan matakin amma daga karshe sun fice daga kasar bayan sojojin sun dage a kan rufe ofishin kungiyar
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
A yau Laraba ne aka bude bikin baje koli karo na 22, na Sin da kasashe membobin kungiyar ASEAN ko (CAEXPO), da kuma taron dandalin kasuwanci da juba jari na Sin da ASEAN ko CABIS, a birnin Nanning na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kai dake kudancin kasar Sin.
A shekarun baya bayan nan, Sin da kungiyar ASEAN, sun ci gaba da cimma manyan nasarori tare a fannin bunkasa dunkulewar tattalin arzikin shiyyarsu, da fadada damar bai daya ta cudanyar mabambantan sassa, a gabar da ake fuskantar yanayin tangal-tangal a duniya.
Wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ta shaida yadda kaso 92.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi suka amince cewa, baje kolin CAEXPO ya bayyana yadda Sin da kungiyar ASEAN suka himmatu wajen bunkasa bude kofa bisa matsayin koli, da kare tsarin cinikayya cikin ’yanci da kasancewar mabambantan sassa.
Kafar CGTN ta gabatar da kuri’ar ne da harsunan Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da yaren Rasha, inda kuma mutane 6,260 suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’ao’i 24. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp