‘Yan Tawayen Sudan Sun Kai Hare-Hare Kan Ayarin Motocin Agaji A Kan Hanyarsu Ta Kai Agajin Jin Kai
Published: 10th, June 2025 GMT
Gwamnatin Sudan ta zargi ‘yan tawayen kasar na dakarun kai daukin gaggawa da kai hari kan ayarin motocin agaji kai a yankin Darfur
Gwamnatin Sudan ta sanar da cewa: “Dakarun kai daukin gaggawa sun kai hari kan ayarin motocin agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a yankin Darfur ta Arewa ta hanyar jiragen sama marasa matuka ciki.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin Sudan ta bayyana matukar bacin ranta tare da tofin Allah tsine da Allah wadai kan wannan mummunan lamari, tana mai jaddada cewa: “Yunkuri ne na ganganci na nufin toshe kungiyoyin agaji da dakile ayyukansu na kai kayan agaji ga fararen hula da suka makale a birnin El Fasher da sansanonin gudun hijira.”
Sanarwar ta ce “Hare-haren masu laifi sun yi sanadin lalata wasu manyan motocin Majalisar Dinkin Duniya, da kashe wasu masu gadi, da direbobi, da fararen hula, da kuma jikkata wasu jami’an tsaro da ke tare da ayarin motocin.”
Gwamnatin Sudan ta tabbatar da cewa: Harin ya saba wa dokokin jin kai na kasa da kasa, kuma kai tsaye da gangan ne aka niyyar illa ga kokarin da gwamnati take yi, tare da hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin kasa da kasa, na kai agajin gaggawa ga fararen hula da ke cikin bukata a halin yakin basasar kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.
Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuShirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.
Domin sauke shirin, latsa nan