Gwamnatin Sudan ta zargi ‘yan tawayen kasar na dakarun kai daukin gaggawa da kai hari kan ayarin motocin agaji kai a yankin Darfur

Gwamnatin Sudan ta sanar da cewa: “Dakarun kai daukin gaggawa sun kai hari kan ayarin motocin agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a yankin Darfur ta Arewa ta hanyar jiragen sama marasa matuka ciki.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin Sudan ta bayyana matukar bacin ranta tare da tofin Allah tsine da Allah wadai kan wannan mummunan lamari, tana mai jaddada cewa: “Yunkuri ne na ganganci na nufin toshe kungiyoyin agaji da dakile ayyukansu na kai kayan agaji ga fararen hula da suka makale a birnin El Fasher da sansanonin gudun hijira.”

Sanarwar ta ce “Hare-haren masu laifi sun yi sanadin lalata wasu manyan motocin Majalisar Dinkin Duniya, da kashe wasu masu gadi, da direbobi, da fararen hula, da kuma jikkata wasu jami’an tsaro da ke tare da ayarin motocin.”

Gwamnatin Sudan ta tabbatar da cewa: Harin ya saba wa dokokin jin kai na kasa da kasa, kuma kai tsaye da gangan ne aka niyyar illa ga kokarin da gwamnati take yi, tare da hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin kasa da kasa, na kai agajin gaggawa ga fararen hula da ke cikin bukata a halin yakin basasar kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.

Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces