Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
Published: 10th, June 2025 GMT
A yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira ga Sin da Korea ta Kudu da su daukaka dangantakarsu zuwa matsayi na gaba ta yadda al’ummominsu za su kara amfana da ita da kawo tabbaci ga duniya mai cike da rashin tabbas, yayin da yake taya Lee Jae-myung murnar lashe zaben shugabancin kasar.
Tabbas kyakkayawar alaka tsakanin Sin da Korea ta kudu ta dace da yanayin da duniya ke ciki da muradun al’ummomin kasashen da ma tabbatuwar zaman lafiya a yankinsu da ma duniya baki daya.
Kamar yadda shugaba Xi ya bayyana, kasashen biyu makwabta ne da ba za a iya raba su ba. Don haka, ci gaban kowacce daga cikinsu, ci gaba ne ga dayar, haka ma akasinsa. Babu wanda yake kin cudanyar kasa da kasa, amma ya kamata, kowacce ’yantacciyar kasa ta kasance mai ra’ayinta na kashin kai da duba moriyarta da na makwabtanta yayin da take hulda da kasashen waje. Tarihi ya nuna yadda daidaituwar al’amura tsakanin bangarorin biyu ke samun tagomashi yayin da rashinsa ke haifar da koma baya. Yayin da Korea ta Kudu ta samu sabon shugaba, fatan ita ce zai jagoranci kasar wajen tsayawa kan ra’ayi na gaskiya da girmamawa da daidaito yayin cudanya da kasar Sin maimakon ba da dama ga masu wani ra’ayi na son kai don amfani da ita da zummar cimma burinsu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
A wani taron sauraron bayanai da aka gudanar a kwanan baya, ‘yar majalisar wakilan kasar Amurka Madeleine Dean ta yi wa ministan kasuwanci na kasar, Howard Lutnick tambayoyi game da yanayin ciniki da manufofin harajin kwastam na kasar, inda ta tono shirmen da ke cikin matakan haraji da Amurka ta dauka a kan kayayyakin da take shigarwa daga kasa da kasa. Kasancewar ayaba tana girma ne a sassa masu zafi, galibin yankunan kasar Amurka ba su dace da nomansu ba. Ko a jihohin Hawaii da Florida da sauran sassan kasar Amurka da suka fi zafi ma, yawan ayabar da ake samarwa ba zai iya biyan bukatun kasuwannin Amurka ba, sabo da wasu dalilai na yanayi da kasuwanci.
A hakika, a yayin da tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen duniya ke kara dunkulewa baki daya, kasa da kasa su kan samu mabambantan fifiko a sana’o’i daban daban sakamakon bambancin albarkatun da suke da su, ko kuma bambancin ci gabansu, lamarin da ya sa suke yin musayar kayayyakin da suke da fifikonsu don tabbatar da bunkasa ta bai daya, hakan nan kuma sana’o’i daban daban na dogara ga juna. Kamar yadda sauran kasashen duniya suke, kasar Amurka ita kanta ta amfana da bunkasuwar tattalin arzikin duniya da kuma ciniki mai ‘yanci.
Duk da haka, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauki matakan haraji na barkatai a yunkurin daidaita matsalar da ya kira wai “gibin kudin ciniki”, matakin da ba haifar da munanan matsalolin haraji a fadin duniya kawai ya yi ba, har da daga farashin kayayyaki a cikin kasar kansa. Lallai Amurka tana fama da rashin lafiya, amma ta sa sauran kasashe shan magani. Hakan ba zai taimaka ga daidaita matsalolin da tsarin tattalin arzikin kasar ke haifarwa ba, sai ma kara tsunduma shi cikin mawuyacin yanayin tattalin arziki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp