IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so
Published: 10th, June 2025 GMT
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa, a halin yanzu Jamhuriyar Musulunci za ta iya kai wa Isra’ila hari “daidai” inda ta ke so bayan samun bayanan sirri kan cibiyoyin nukiliyar gwamnatin Isra’ila.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wata wasika mai zuwa ga ministan leken asirin kasar, Esmail Khatib, inda ya taya shi murnar wani samame da aka kai a kwanan baya wanda ya bayar da damar samun bayyana sirrin Isra’ila da dama kan shirinta na nukiliya.
Wannan nasarar, ta baiwa hukumomin leken asirin Iran damar samun wasu tarin takardun Isra’ila da suka shafi makaman nukiliya, soji, tsaro da wasu wurare na kayayyakin more rayuwa.
Wuraren sun hada da wuraren da Isra’ila ke da shirin nukiliyar gwamnatin na boye, wanda aka ce ya baiwa Tel Aviv damar kera daruruwan makamai masu linzami da ba a san da su ba.
Janar Salami ya kara da cewa: “Wadannan takardun sirrin babu shakka zasu inganta tasirin kokarin da ake yi na hanzarta kawar da gwamnatin Sahayoniyawan da kuma kara sahihancin harin makamai masu linzami na Iran.
A shekarar da ta gabata Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kai hari kan wasu muhimman wurare na Isra’ila a yankunan Falasdinawa da ta mamaye a wani gagarumin farmakin ramuwar gayya da ta gudanar a matsayin mayar da martani ga wuce gona da iri na gwamnatin Isra’ila.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura
Shugaban Ƙasar Gambiya, Adama Barrow, tare da matarsa Fatoumata Barrow, sun ziyarci Jihar Katsina, inda suka yi ta’aziyyar rasuwar tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari.
Sun kai ziyarar ne a ranar Juma’a domin jajanta wa iyalan marigayin game da rashin da suka yi.
Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasarSun sauka a filin jirgin sama na Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, inda Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Barista Abdullahi Faskari, ya tarbe su a madadin Gwamna Dikko Umar Radda.
Bayan sojoji sun yi wa Shugaba Barrow faretin ban girma, sun wuce Daura kai-tsaye, inda suka yi wa iyalan marigayin da kuma Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk ta’aziyya.
Ga hotunan a ƙasa: