IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so
Published: 10th, June 2025 GMT
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa, a halin yanzu Jamhuriyar Musulunci za ta iya kai wa Isra’ila hari “daidai” inda ta ke so bayan samun bayanan sirri kan cibiyoyin nukiliyar gwamnatin Isra’ila.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wata wasika mai zuwa ga ministan leken asirin kasar, Esmail Khatib, inda ya taya shi murnar wani samame da aka kai a kwanan baya wanda ya bayar da damar samun bayyana sirrin Isra’ila da dama kan shirinta na nukiliya.
Wannan nasarar, ta baiwa hukumomin leken asirin Iran damar samun wasu tarin takardun Isra’ila da suka shafi makaman nukiliya, soji, tsaro da wasu wurare na kayayyakin more rayuwa.
Wuraren sun hada da wuraren da Isra’ila ke da shirin nukiliyar gwamnatin na boye, wanda aka ce ya baiwa Tel Aviv damar kera daruruwan makamai masu linzami da ba a san da su ba.
Janar Salami ya kara da cewa: “Wadannan takardun sirrin babu shakka zasu inganta tasirin kokarin da ake yi na hanzarta kawar da gwamnatin Sahayoniyawan da kuma kara sahihancin harin makamai masu linzami na Iran.
A shekarar da ta gabata Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kai hari kan wasu muhimman wurare na Isra’ila a yankunan Falasdinawa da ta mamaye a wani gagarumin farmakin ramuwar gayya da ta gudanar a matsayin mayar da martani ga wuce gona da iri na gwamnatin Isra’ila.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bam Ya Hallaka Masu Yawon Sallah A Sakkwato
A baya, irin wannan mummunan abu ya faru a yankin, inda sojoji da dama suka rasa rayukansu sakamakon fashewar bama-bamai.
Hakan na ƙara nuna irin barazanar da matsalar tsaro ke ci gaba da haifarwa a Jihar Sakkwato, inda mazauna ke roƙon gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen kawo ƙarshen hare-haren ‘yan ta’adda, musamman masu tayar da bama-bamai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp