Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gabatar da jawabi ta bidiyo a gun bikin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” karo na farko na MDD yau Talata.

Wang Yi ya bayyana cewa, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shirin raya al’adu na duniya, inda ya ba da shawarar raya dabi’u na bai daya na dukkan bil’adama, da dora muhimmanci kan gado da kirkire-kirkire na wayewar kai, da karfafa mu’amala da hadin gwiwar al’adu tsakanin kasa da kasa, wadanda muhimmin kokari ne da kasar Sin ta yi don inganta tattaunawa tsakanin wayewar kai.

A shekarar 2024, babban taron MDD karo na 78, ya amince da kudurin da kasashe 83 ciki har da kasar Sin suka gabatar, na tabbatar da ranar 10 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa”. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe

Babbar Kotun Jiha a Gombe mai lamba ta 3 ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu mutum uku bisa laifin haɗa baki da kuma kisan kai.

Alƙalin kotun Mai shari’a Haruna Kereng ne ya jagoranci shari’ar, inda ya ce kotu ta sami Dauda Mohammed Abubakar (wanda aka fi sani da Agenda) da Kabiru Abubakar (Gwarei) da Ibrahim Suleiman da laifi a kan dukkanin tuhume-tuhumen da ake musu dangane da kisan Ibrahim Yahaya a unguwar Herwagana da ke Ƙaramar Hukumar Gombe a ranar 22 ga Afrilu, 2022.

An kai hari a ƙauyuka uku da kashe mutum 7 a Imo An kashe mata da yara a sabon harin Filato

Kotun ta ji cewa, mutanen ukun sun kai wa Ibrahim Yahaya hari ɗauke da makamai masu haɗari kamar: takubba da wuƙa, inda suka kashe shi tare da jikkata wasu mutane biyu, wato Ahmed Abubakar da Muhammad Ahmed Lawan a lokacin harin.

Shari’ar ta fara tun ranar 17 ga watan Nuwamba, 2022, kuma an kammala ta a ranar Laraba, 24 ga Yuli, 2025.

Kereng ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjoji masu ƙarfi da suka tabbatar da laifin da waɗanda ake tuhuma suka aikata, kamar yadda doka ta tanada a sashe na 97 da 221 na dokar laifuka, wanda ta tanadar da hukuncin kisa ga wanda aka same shi da laifin haɗa baki da kuma kisan kai.

Yayin da yake yanke hukunci, Mai sharia Kereng ya ce “Kowannen ku za a rataye shi a wuyansa har sai an tabbatar da mutuwarsa ta hanyar gwajin likita.”

Ya kara da cewa kotu ba ta da ikon rage hukuncin, don haka ba ta saurari roƙon sassauci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
  • Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
  • Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
  • Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka
  • Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
  • Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin