HausaTv:
2025-06-22@18:24:07 GMT

Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya

Published: 10th, June 2025 GMT

Ma’aikatar tsaron ta Amurka ta sanar da cewa za ta baza zaratan sojojin kasar na “Marines” akan titunan birnin Los Angeles domin fuskantar tashe-tashen hankulan da ake yi domin hana korar ‘yan ci-rani  ba bisa ka’ida ba.

Sanarwar ma’aikata tsaron kasar ta ce; Tuni na shirya sojojin na “Marines” 700 domin su yi aikli da rundunar “National Guards” wacce tuni tana kan titunan birnin bisa umarnin shugaba Donald Trump domin kama ‘yan hijira ba bisa ka’ida ba.

Ministan tsaron kasar ta Amurka  ya ce ; za a kai sojojin ne a cikin birnin saboda bayar da kariya ga muhimman gine-ginen gwamnatin tarayya da kuma dawo da doka da oda.

Shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya fada a jiya cewa, ba manufarsa ganin yakin basasa ya barke a Amurka ba, amma kuma ya yi wa masu tayar da kayar baya a cikin birnin Los Angeles barazanar dandana kudarsu saboda yadda suke cutar da rundunar kasa ( National Guards.)

A gefe daya gwamnan Jahar ta California Gavin Christopher dan jam’iyyar Democrat ya yi suka da kakkausar murya akan Shirin aikewa da zaratan sojojin na Amurka akan titunan birnin Los Angelos, yana mai cewa bai kamata a kai sojoji a cikin titunan Amurka ba.

Gwamnan ya kara da cewa; Aikewa da sojoji zuwa titunan California, wani kokari ne na Trump domin kara raba kan al’ummar kasar.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna baƙin cikinsa kan kisan wasu matafiya daga Jihar Kaduna da aka yi a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Matafiyan sun fito ne daga Zariya suna kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure, yayin da wasu ɓata-gari suka farmake su.

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani

Gwamnan ya ce wannan kisa abin takaici ne kuma rashin imani ne da ya saɓa wa doka.

Ya buƙaci a yi adalci cikin gaggawa.

Haka kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kaduna, iyalan mamatan, da sauran waɗanda abin ya shafa.

A cewar sanarwar da Daraktan Yaɗa Labaran Gwamnatin Jihar Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, Gwamna Yahaya ya yaba wa gwamnati da ‘yan sanda a Jihar Filato bisa kamo wasu da ake zargi da hannu a kisan.

Gwamnan ya buƙaci a yi bincike na gaskiya, a gurfanar da waɗanda ke da hannu domin a hukunta su, sannan a hana irin hakan faruwa a gaba.

Haka kuma, ya roƙi al’ummar Filato da Kaduna da sauran maƙwabta da su zauna lafiya, su guji ɗaukar fansa.

Ya ce Gwamnonin Arewa za su ci gaba da haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

“Ina tabbatar muku cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban burinmu. Za mu yi aiki tare har sai an kawo ƙarshen wannan matsala,” in ji Gwamnan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya