HausaTv:
2025-12-10@14:59:34 GMT

Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya

Published: 10th, June 2025 GMT

Ma’aikatar tsaron ta Amurka ta sanar da cewa za ta baza zaratan sojojin kasar na “Marines” akan titunan birnin Los Angeles domin fuskantar tashe-tashen hankulan da ake yi domin hana korar ‘yan ci-rani  ba bisa ka’ida ba.

Sanarwar ma’aikata tsaron kasar ta ce; Tuni na shirya sojojin na “Marines” 700 domin su yi aikli da rundunar “National Guards” wacce tuni tana kan titunan birnin bisa umarnin shugaba Donald Trump domin kama ‘yan hijira ba bisa ka’ida ba.

Ministan tsaron kasar ta Amurka  ya ce ; za a kai sojojin ne a cikin birnin saboda bayar da kariya ga muhimman gine-ginen gwamnatin tarayya da kuma dawo da doka da oda.

Shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya fada a jiya cewa, ba manufarsa ganin yakin basasa ya barke a Amurka ba, amma kuma ya yi wa masu tayar da kayar baya a cikin birnin Los Angeles barazanar dandana kudarsu saboda yadda suke cutar da rundunar kasa ( National Guards.)

A gefe daya gwamnan Jahar ta California Gavin Christopher dan jam’iyyar Democrat ya yi suka da kakkausar murya akan Shirin aikewa da zaratan sojojin na Amurka akan titunan birnin Los Angelos, yana mai cewa bai kamata a kai sojoji a cikin titunan Amurka ba.

Gwamnan ya kara da cewa; Aikewa da sojoji zuwa titunan California, wani kokari ne na Trump domin kara raba kan al’ummar kasar.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi

An kori direban Kamfanin Simintin Mangal bayan jami’an tsaro sun kama shi da motar kamfanin dauke da yara 21 da ake zargin an yi safarar su ne daga jihohin Arewa.

Gwamnatin jihar ta ce yaran da ke tsakanin shekaru 6 zuwa 17 an kama su ne bisa sahihan bayanan sirri.

Sanawar da Kwamishinan Yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar bayan kama yaran a cikin motar ta yi zargin za a yi amfani da su wajen horar da ’yan ta’adda.

Kamfanin ya nesanta kansa daga lamarin, ya ce direban ya karya dokokin aiki, kuma ya jefa al’umma cikin haɗari.

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Babban Manajan sashin kula da mulki na kamfanin, Musa Umar, ya ce ba da izininsa direban da aka kama ya fita da motar ba, domin iya jigilar siminta kaɗai suke yi ba ɗaukar fasinja ko yara ba.

Gwamnatin Kogi ta ce za a mika yaran ga gwamnatocin jihohinsu bayan tantancewa, yayin da duk wanda aka samu da hannu a safarar zai fuskanci shari’a bisa dokokin hana safarar yara da kare haƙƙin yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila