Aminiya:
2025-09-17@21:51:06 GMT

Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa

Published: 8th, June 2025 GMT

Aƙalla mutum tara ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a ƙauyen Kyaramma da ke Ƙaramar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Asabar, inda motoci biyu ƙirar Golf 3 suka yi taho-mu-gama, kuma mutane da dama sun jikkata.

Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya  Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah

Ɗaya daga cikin motocin, mai lambar Kaduna MKA 687 AY, ana ɗauke da ita ne daga Abuja zuwa garin Gujungu, kuma direban motar mai suna Adamu Sunusi, mai shekaru 35 daga Ƙaramar Hukumar Hadeja.

Rahoton ’yan sanda ya nuna cewa hatsarin ya faru ne bayan ɗaya daga cikin direbobin motarsa ta ƙwace masa, wanda hakan ya sa motocin biyu suka yi karo da juna.

’Yan sanda sun isa wajen, kuma sun garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Ringim domin kula da su.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP A.T. Abdullahi, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya yi addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.

Ya kuma shawarci direbobi da su riƙa bin dokokin hanya, su guji gudu fiye da ƙima, tare da tabbatar da cewa motocinsu na cikin ƙoshin lafiya kafin su hau hanya.

Ya bayyana cewa mutum 11 da suka jikkata suna asibiti inda ake kula da su, kuma suna samun sauƙi.

Yanzu haka ana ci gaba da gano sunayen waɗanda lamarin ya shafa da kuma sanar da iyalansu.

’Yan sanda sun ce za su ci gaba da fitar da bayanai yayin da bincike ke gudana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda hatsarin mota Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025

Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.

Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.

Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Shugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.

Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.

Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.

Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.

Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.

Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.

NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.

Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.

Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.

Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara