Aminiya:
2025-06-19@18:49:33 GMT

Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa

Published: 8th, June 2025 GMT

Aƙalla mutum tara ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a ƙauyen Kyaramma da ke Ƙaramar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Asabar, inda motoci biyu ƙirar Golf 3 suka yi taho-mu-gama, kuma mutane da dama sun jikkata.

Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya  Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah

Ɗaya daga cikin motocin, mai lambar Kaduna MKA 687 AY, ana ɗauke da ita ne daga Abuja zuwa garin Gujungu, kuma direban motar mai suna Adamu Sunusi, mai shekaru 35 daga Ƙaramar Hukumar Hadeja.

Rahoton ’yan sanda ya nuna cewa hatsarin ya faru ne bayan ɗaya daga cikin direbobin motarsa ta ƙwace masa, wanda hakan ya sa motocin biyu suka yi karo da juna.

’Yan sanda sun isa wajen, kuma sun garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Ringim domin kula da su.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP A.T. Abdullahi, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya yi addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.

Ya kuma shawarci direbobi da su riƙa bin dokokin hanya, su guji gudu fiye da ƙima, tare da tabbatar da cewa motocinsu na cikin ƙoshin lafiya kafin su hau hanya.

Ya bayyana cewa mutum 11 da suka jikkata suna asibiti inda ake kula da su, kuma suna samun sauƙi.

Yanzu haka ana ci gaba da gano sunayen waɗanda lamarin ya shafa da kuma sanar da iyalansu.

’Yan sanda sun ce za su ci gaba da fitar da bayanai yayin da bincike ke gudana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda hatsarin mota Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Aiki ceton, ya samu hadin gwiwar kungiyoyin ceto da suka hada da Red Cross da Hukumar Kula da Ruwan Kogin (NIWA) da jama’ar garin Yauri.

 

A ranar Laraba, an yi jana’izar Mutane uku, a garin Hikiya da ke karamar hukumar Rohiya a jihar Neja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri
  • HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga