Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa
Published: 8th, June 2025 GMT
Aƙalla mutum tara ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a ƙauyen Kyaramma da ke Ƙaramar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.
Rundunar ’yan sandan jihar, ta ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Asabar, inda motoci biyu ƙirar Golf 3 suka yi taho-mu-gama, kuma mutane da dama sun jikkata.
Ɗaya daga cikin motocin, mai lambar Kaduna MKA 687 AY, ana ɗauke da ita ne daga Abuja zuwa garin Gujungu, kuma direban motar mai suna Adamu Sunusi, mai shekaru 35 daga Ƙaramar Hukumar Hadeja.
Rahoton ’yan sanda ya nuna cewa hatsarin ya faru ne bayan ɗaya daga cikin direbobin motarsa ta ƙwace masa, wanda hakan ya sa motocin biyu suka yi karo da juna.
’Yan sanda sun isa wajen, kuma sun garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Ringim domin kula da su.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP A.T. Abdullahi, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya yi addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.
Ya kuma shawarci direbobi da su riƙa bin dokokin hanya, su guji gudu fiye da ƙima, tare da tabbatar da cewa motocinsu na cikin ƙoshin lafiya kafin su hau hanya.
Ya bayyana cewa mutum 11 da suka jikkata suna asibiti inda ake kula da su, kuma suna samun sauƙi.
Yanzu haka ana ci gaba da gano sunayen waɗanda lamarin ya shafa da kuma sanar da iyalansu.
’Yan sanda sun ce za su ci gaba da fitar da bayanai yayin da bincike ke gudana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda hatsarin mota Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin sallar Idi Al-Adha A Tehran Ya Jaddada Cewa: Imam Khomeini {r.a} Ya Kawo Sauyi Da Ci Gaba A Iran
Limamin da ya jagoranci Sallar Idi Al-Adha a Tehran ya bayyana cewa: Imam Khumaini (r.a) ya kawo sauyi mai girma da fadi a Iran
Limamin da ya jagoranci Sallar Idin Al-Adha a birnin Tehran Hujjatul-Islam Hasan Abu Torabi Fard ya bayyana cewa: Imam Khumaini (r.a) ya share fagen kasancewar al’ummar Iran a fagage mafi muhimmanci na yanke shaawara, sannan kuma ya ba da damar samun gagarumin sauyi mai girma a Iran.
Hujjatul- Islam Abu Torabi Fard ya kara da cewa: Muna tunawa da rasuwar wani fitaccen mutum kuma fitaccen mutum wanda ya taso kuma aka rene shi a cikin mazhabar hankali da ilimi da tauhidi na ubangijinmu Ibrahim Majibin Rahma (amincin Allah ya tabbata a gare shi).
Ya ci gaba da cewa: Imam Khumaini (r.a) ta hanyar samar da ginshiki na tabbatar da hankali da tasiri ga mutane a fagagen yanke shawara mafi muhimmanci da kuma fitattun bangarori na siyasa da zamantakewar al’umma.