Tarzoma ta barke a sassan Amurka da dama, har ta kai shugaban kasar ya bayar da umarnin kama gwamna. An kuma jibge dubban sojoji a birnin Los Angeles, kamar dai yadda jaridar “The Mirror” ta bayyana.

Wani sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta fitar, ya nuna kaso mai yawa na Amurkawa sun damu da yiwuwar barkewar yakin basasa a kasar.

Sakamakon kuri’un jin ra’ayoyin ya nuna cewa, kaso 78.3 bisa dari na ganin a matsayin Amurka ta kasa da ta ginu bisa hadakar bakin haure, kuma a yanzu take aiwatar da akidun yaki da bakin haure, hakan ya saba wa matakan bunkasar kasar bisa tarihi, zai kuma illata alkiblar ci gabanta a nan gaba.

Bisa alkaluman jin ra’ayin al’umma, kaso 87 bisa dari na masu bayyana mahangarsu sun soki lamirin gwamnatin Amurka, bisa yadda take keta hakkokin bil’adama yayin da take tunkarar batun bakin haure. Kazalika, kaso 86 bisa dari na ganin batun bakin haure ya zamo wata babbar matsala ga tsarin jagorancin Amurka a cikin gida. Yayin da kaso 73.8 bisa dari ke ganin la’akari da tsanantar yanayin siyasa, da karuwar gibin tsakanin mawadata da talakawa, rayuwar Amurkawa marasa wadata tana kara tsananta. Har ma suna ganin an zuzuta zargin cewa wai bakin haure dake shiga Amurka ba bisa ka’ida ba sun fantsama a sassan kasar, yayin da kuma sabbin bakin haure dake shiga Amurka ke fuskantar kyama, sakamakon rikicin cikin gida dake ruruwa a kasar. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa nasarar da tawagar ƙwallon ƙafa ta mata ta Nijeriya (Super Falcons) ta samu a gasar cin kofin Afrika na mata (WAFCON) 2025, inda ya ce yana sa ran karɓar kofin daga hannunsu a Abuja.

A cikin wata hira ta bidiyo da aka yi da shugaban ƙasa jim kaɗan bayan wasan, tare da kyaftin din tawagar, Rasheedat Ajibade, da wasu ‘yan wasan da jami’an tawagar, Tinubu ya taya su murna bisa lashe kofin karo na 10. Ya ce wannan nasara wata hanya ce da ke ɗaukaka darajar Nijeriya a idon duniya.

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata  Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

“Ina alfahari da ku, Nijeriya gaba ɗaya na alfahari da ku. Kun ɗaga martabar ƙasarmu, ku abin koyi ne a zamanin ku. Ina mika godiya ta musamman ga masu horar da tawagar,” in ji Tinubu, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar. Shugaban ya kuma miƙa saƙon ban girma ga Rasheedat Ajibade da ta samu lambar gwarzon ‘yar wasa a gasar.

Yayin da yake zantawa da tawagar, Tinubu ya yi addu’ar dawowar su lafiya zuwa gida, yana cewa: “Ina fatan zaku iso lafiya, Allah ya saka muku da alheri.” A madadin tawagar, Rasheedat ta gode wa shugaban ƙasa bisa amincewa da biyan cikakken alawus na ‘yan wasan, tana mai tabbatar masa da cewa tawagar za ta ba da dukkan ƙoƙarinta wajen kawo kofin WAFCON zuwa Abuja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
  • Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
  • Kasar Iran Ta Ce Tana Hulda Da Amurka Ta Hanyar Masu Shiga Tsakani
  • An Fara Zaman Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Sauya Kundin Tsarin Mulki A Kano
  • Musulmi A Amurka Sun Fara Daukar Matakan Tsaro A Masallatai Saboda Makiya
  • Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba
  • Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa