Tarzoma ta barke a sassan Amurka da dama, har ta kai shugaban kasar ya bayar da umarnin kama gwamna. An kuma jibge dubban sojoji a birnin Los Angeles, kamar dai yadda jaridar “The Mirror” ta bayyana.

Wani sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta fitar, ya nuna kaso mai yawa na Amurkawa sun damu da yiwuwar barkewar yakin basasa a kasar.

Sakamakon kuri’un jin ra’ayoyin ya nuna cewa, kaso 78.3 bisa dari na ganin a matsayin Amurka ta kasa da ta ginu bisa hadakar bakin haure, kuma a yanzu take aiwatar da akidun yaki da bakin haure, hakan ya saba wa matakan bunkasar kasar bisa tarihi, zai kuma illata alkiblar ci gabanta a nan gaba.

Bisa alkaluman jin ra’ayin al’umma, kaso 87 bisa dari na masu bayyana mahangarsu sun soki lamirin gwamnatin Amurka, bisa yadda take keta hakkokin bil’adama yayin da take tunkarar batun bakin haure. Kazalika, kaso 86 bisa dari na ganin batun bakin haure ya zamo wata babbar matsala ga tsarin jagorancin Amurka a cikin gida. Yayin da kaso 73.8 bisa dari ke ganin la’akari da tsanantar yanayin siyasa, da karuwar gibin tsakanin mawadata da talakawa, rayuwar Amurkawa marasa wadata tana kara tsananta. Har ma suna ganin an zuzuta zargin cewa wai bakin haure dake shiga Amurka ba bisa ka’ida ba sun fantsama a sassan kasar, yayin da kuma sabbin bakin haure dake shiga Amurka ke fuskantar kyama, sakamakon rikicin cikin gida dake ruruwa a kasar. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar

Ministan man fetur na kasar Iran Mohsen Paknejad ya bayyana cewa kasarsa zata ci gaba da saida danyen man fetur ga masu sayensa a kasashen waje duk tare da kokarin gwamnatin kasar Amurka na kara kuntatawa kasar a bangaren saida makamashin kasar ga kasashen waje.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya laraba bayan taron majalisar ministocin kasar a nan Tehran.

Ministan ta kara da cewa shirin Amurka na hana Iran saida danyen manta ga kasashen waje zai rugurguje kamar yadda ya rugurguje a baya. Y ace don mun rika mun gano kan zaren lalata duk wani shiri na hana mu saida danyin man ga masu sayan man kasar.

Ministan ya bayyana cewa labara ya zo masa kan cewa gwamnatin Amurka na kokarin kakabawa kasar takunkuman tattalin arziki kan sinadarin Methanol na kasar, shi ma suna aiki a kansa.

Gwamnatin Amurka ta Donal Trump tun watan Fabray run wannan shekarar ta fara wani sabin shiri na takurawa Iran, daga ciki har da maida sayar da danyen man fetur na kasar zuwa sifili.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro
  • Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi
  • Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center
  •  Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza