Wani Kamfanin Kera Kayankin Aikin Likita Ya Gabatar Da Sabon Na’urar Tiyata
Published: 10th, June 2025 GMT
Wani kamfanin kera kayakin aikin likita mai zaman kansa a nan Tehran ya gabatar da wata na’ura mai aikin tiyata wanda kuma aka dora masa kayan aiki na zamani.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa an gabatara da wannan na’urar a kasuwar baje kolin kayakin aikin likita karo na 26TH wanda ke gudana a nan birnin Tehran.
Labarin ya kara da cewa samar da kayalin aikin likita wadanda suke tafiya da zamani, ya zama dole ne bayanda aka haka sayarwa kasar Iran irinsu daga waje.
Wannan hanin ya sa a dole daga cikin gida kwararru suka fara samar da kayakin aikin likita na zamani, don wadatar da asbitocin kasar daga sayan na waje, har ma tana sayarwa kasashen waje.
Mostafa Abdulgaffar shugaban kamfanin da ya samar da wannan na’urar yace : Na’urar za ta taimakawa lokitoci da wasu ayyuka masu muhimmanci dangane da marasa lafiyan da sukewa aiki, ta yadda likitocin ba za su yi kuskure na bata wani wuri a cikin jikin marasa lafiya wanda sukewa aiki ba.
Abdulgaffar ya kara da cewa kafin haka kasar Iran tana shigo da irin wadannan kayakin aikin likita ne daga kasashen Amurka, da Jamus. Amma bayan an dorawa kasar takunkuman tattalin arziki, sun dukufa a cikin gida saida suka samar da su. Suka kuma sami lasicin aiki da su a cikin asbitocin kasar da kuma saida su ga kasashen waje.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kayakin aikin likita
এছাড়াও পড়ুন:
A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alou — Gwamnatin Borno
Gwamnatin Jihar Borno ta yi kira ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta hanzarta ɗaukar mataki kan ɗan kwangilar da ta baiwa aikin yashe dam ɗin Alou da ya haifar da ambaliya a bara.
Ta ce duk da cewar sun yashe wani sashe na dam din amma, har yanzu akwai babbar barazana da za a iya fuskantar mummunar ambaliya.
Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya Saudiyya za ta fara bayar da bizar UmaraKwamishinan yaɗa labarai da harkokin tsaro na Jihar Borno, Farfesa Umar Tar da harkokin tsaro ya shaida wa BBC cewa an bayar da kwantaragin kuma minista ya je ya ƙaddamar da aikin.
“Har yanzu ba mu ga ’yan kwangila sun zo domin fara aikin ba kuma yanzu ga damuna ta riga ta sauka.
“Idan ba a yi aikin nan da wuri ba to idan ruwa ya zo ya yi halinsa to lallai za a samu matsala.
“Ya kamata a ce an yashe ruwan saboda irin cunkushewar da ya yi. Idan aka yashe shi to ko ruwa ya zo da yawa ba zai ambaliya ba,” in ji Farfesa Tar.
A damunar bara ne dai madatsar ruwa ta Alou Dam ta cika ta tunbatsa inda ta kuma karye, wani abu da ya janyo ambaliyar ruwa da ya haddasa asarar rayuka da ta dukiyoyi a birnin Maiduguri.