HausaTv:
2025-12-08@04:01:12 GMT

Wani Kamfanin Kera Kayankin Aikin Likita Ya Gabatar Da Sabon Na’urar Tiyata

Published: 10th, June 2025 GMT

Wani kamfanin kera kayakin aikin likita mai zaman kansa a nan Tehran ya gabatar da wata na’ura mai aikin tiyata wanda kuma aka dora masa kayan aiki na zamani.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa an gabatara da wannan na’urar a kasuwar baje kolin kayakin aikin likita karo na 26TH wanda ke gudana a nan birnin Tehran.

Labarin ya kara da cewa samar da kayalin aikin likita wadanda suke tafiya da zamani, ya zama dole ne bayanda aka haka sayarwa kasar Iran irinsu daga waje.

Wannan hanin ya sa a dole daga cikin gida kwararru suka fara samar da kayakin aikin likita na zamani, don wadatar da asbitocin kasar daga sayan na waje, har ma tana sayarwa kasashen waje.

Mostafa Abdulgaffar shugaban kamfanin da ya samar da wannan na’urar yace : Na’urar za ta taimakawa lokitoci da wasu ayyuka masu muhimmanci dangane da marasa lafiyan da sukewa aiki, ta yadda likitocin ba za su yi kuskure na bata wani wuri a cikin jikin marasa lafiya wanda sukewa aiki ba.

Abdulgaffar ya kara da cewa kafin haka kasar Iran tana shigo da irin wadannan kayakin aikin likita ne daga kasashen Amurka, da Jamus. Amma bayan an dorawa kasar takunkuman tattalin arziki, sun dukufa a cikin gida saida suka samar da su. Suka kuma sami lasicin aiki da su a cikin asbitocin kasar da kuma saida su ga kasashen waje.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kayakin aikin likita

এছাড়াও পড়ুন:

Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi

Fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Ahmad Mahmud Abubakar Gumi, ya yi zargin cewa ƙasashen waje na taimaka wa ƙungiyoyin ’yan ta’adda Najeriya.

Sheikh Ahmad Gumi ya danganta ƙaruwar matsalar tsaro a Najeriya a baya-bayan nan da irin maganganun da ƙasashen waje suka riƙa yi a kai.

A yayin wata hira da BBC Hausa, malamin ya bayyana cewa yanayin taɓarɓarewar tsaro a baya-bayan nan ya nuna akwai alamun hannun ƙasashen waje a ciki.

Tsohon hafsan sojin, ya ce matsalar tsaro ta ragu a sassan ƙasar nan sai baya-bayan nan da ƙasashen waje suka fara magana a kai.

Ya bayyana cewa an samu aminci a hanyar Abuja zuwa Kaduna, wadda baya ta kasance tarkon mutuwa, amma sai kwanan nan matsalar ta fara dawowa bayan maganganun ƙasashen waje.

Ya ce manoma a yankin Birnin Gwari sun ci gaba harkokin nomansu, bayan samuwar zaman lafiya, abin da ya gare su a baya lokacin da ake ganiyar rashin tsaro.

“Akwai maganar da ƙasashen waje suka yi, kuma mun jima muna cewa ƙasashen waje ke taimak aa ’yan ta’adda da irin muggan makamai da suke amfani da su.
“Akwai attajirai da shugabannin ƙasashen waje da ke yin katsalandan ga harkokin wasu ƙasashe.”

Don haka ya ce ba abin mamaki ba ne samun ƙaruwar hare-haren ta’addanci da aka yi a Najeriya bayan maganganun ƙasashen waje a kan matsalar tsaro a ƙasar.

Kan matsayinsa game da tattaunawa da ’yan bindiga, ya ce:  “Kowa ya san su. Amma abin da mutane ba sa magana a kai shi ne: me ya sa mutanen da muka taɓa rayuwa lafiya da su suka juya mana baya suka zama annoba a cikin al’umma? Akwai dalili.”

“Mutane biyu ne ba za a yi mamakin abin da suke yi ba: mahaukaci da jahili. Babu wani bayani da za ka yi musu da zai sa su fahimci cewa aikata laifi ba daidai ba ne.”

“Babu abin da suka sani face ɓarna. Amma wa zai yi musu nasiha su daina? Lokacin da muka yi ƙoƙarin kusantar su muka gaya musu cewa haramun ne sata, ƙwace dukiyar mutane haramun ne, yin garkuwa da mutane haramun ne, gwamnatin da ta gabata ba ta ba mu goyon baya ba.

“Da an ba da wannan goyon bayan, watakila da zuwa yanzu an warware wannan matsala.”

Sheikh Gumi ya yi gargaɗi cewa muddin ba a magance tushen matsalar ba, to akwai sauran rina a kaba.

Ya kuma ja hankali jama’a su fahimci cewa matakin yaki da ta’addanci da ya ɗauka, musamman neman sulhu da ’yan bindiga ba, ba ya nufin goyon bayan ayyukansu.

“Addininmu ya haramta zalunci; Duk abin da muke yi, muna yi ne domin Allah,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
  • Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda