Ministan harkokin wajen Iran yayi kashedi ga kasashen Turai cewa: Iran za ta mayar da martani ga duk wani matakin kare hakkinta

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gargadi kasashen Turai kan daukar duk wani mummunan mataki kan Iran a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, yana mai jaddada cewa; Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani keta hakkinta.

Abbas Araqchi ya rubuta a ranar Juma’a a cikin wani sakon da ya wallafa a dandalin X cewa: “Maimakon yin aiki da kyakkyawar niyya, Tawagar Turai ta zaɓi ɗaukar munanan matakai kan Iran a kwamitin alkalan hukumar IAEA.” Ya kara da cewa: “Lokacin da wadannan kasashe uku suka rungumi dabi’ar kuskure iri daya a shekara ta 2005, sakamako ne na sabbin al’amura suka fito a fuskoki da dama, ciki har da kai Iran ga gagarumin matsayin inganta sinadarin Uranium a cikin kasarta. Shin har yanzu tawagar kasashen Turai ba su koyi wani darasi ba cikin shekaru ashirin da suka gabata a mu’amalarsu da Iran?” Ya ci gaba da cewa: Zarge-zargen da ake yi kan Iran da tuhumarta da karya yarjejeniyar tsaro – bisa ga rahotanni masu rarrafe da siyasa – a fili yana nufin haifar da neman rikici ne. Turai na gab da sake fuskantar wani babban kuskuren dabarun.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bukaci hadin kan al’ummar kasar Lebanon wajen warware matsalolin kasar, yana mai kira da a yi shawarwarin kasa tsakanin dukkanin kungiyoyin siyasa domin cimma matsaya daya.

Araghchi ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi a ranar Talata, da shugaban kasar Labanon, Joseph Aoun a birnin Beirut.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada aniyar kasarsa na bunkasa alakarta da kasar Lebanon, bisa mutunta juna.

Ya kuma sanar da cewa, kamfanonin Iran a shirye suke su marawa gwamnatin Lebanon baya a kokarinta na sake gina kasar.

A nasa bangaren shugaba Aoun ya jaddada tsarin gwamnatinsa na bunkasa alaka da dukkan kasashen duniya tare da tabbatar da aniyar kasar Lebanon na kara dankon zumuncin da ke tsakaninta da Iran a fannoni daban daban.

Ya jaddada cewa kawo karshen mamayar wasu sassan kasar Lebanon da kuma gyara barnar da gwamnatin Isra’ila ta yi, su ne manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta Labanon ta sa a gaba.

Araghchi ya kuma gana da firaministan kasar Lebanon Nawaf Salam, A yayin wannan ganawar, sun yi musayar ra’ayi kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin.

Araghchi ya bayyana ziyarar tasa a matsayin wani bangare na manufofin gwamnatin Iran na karfafa alaka da kasashe makwabta da na shiyya, ciki har da Lebanon.

Kafin hakan dama ya ziyarci kasar Masar, a ci gaba da wannan manufa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Miliyoyim Musulmi A Nan Iran Da Sauran kasashen Duniya Ne Suka Yi Sallar Idin Layyah
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Sheikh Naim Qassem Da Aragchi Sun Tabbatar Da Kara Karfin Zumunci Tsakanin Iran Da Lebanon
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar