Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
Published: 6th, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran yayi kashedi ga kasashen Turai cewa: Iran za ta mayar da martani ga duk wani matakin kare hakkinta
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gargadi kasashen Turai kan daukar duk wani mummunan mataki kan Iran a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, yana mai jaddada cewa; Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani keta hakkinta.
Abbas Araqchi ya rubuta a ranar Juma’a a cikin wani sakon da ya wallafa a dandalin X cewa: “Maimakon yin aiki da kyakkyawar niyya, Tawagar Turai ta zaɓi ɗaukar munanan matakai kan Iran a kwamitin alkalan hukumar IAEA.” Ya kara da cewa: “Lokacin da wadannan kasashe uku suka rungumi dabi’ar kuskure iri daya a shekara ta 2005, sakamako ne na sabbin al’amura suka fito a fuskoki da dama, ciki har da kai Iran ga gagarumin matsayin inganta sinadarin Uranium a cikin kasarta. Shin har yanzu tawagar kasashen Turai ba su koyi wani darasi ba cikin shekaru ashirin da suka gabata a mu’amalarsu da Iran?” Ya ci gaba da cewa: Zarge-zargen da ake yi kan Iran da tuhumarta da karya yarjejeniyar tsaro – bisa ga rahotanni masu rarrafe da siyasa – a fili yana nufin haifar da neman rikici ne. Turai na gab da sake fuskantar wani babban kuskuren dabarun.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
Sakatare-janar na kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qasem ya fitar da wata sanarwa inda ya yi kakkausar suka da Allah wadai da abin da ya bayyana a matsayin yakin kisan kare dangi da Amurka da Isra’ila ke yi wa al’ummar Palasdinu a Gaza, yana mai zargin kasashen duniya da yin shiru a kan laifukan da suka zarce dukkan matakan jin kai da kuma kyawawan dabi’u na ‘yan adataka.
“Abin da al’ummar Falasdinawan da ake zalunta ke jurewa a Gaza, tun daga cin zarafi na Amurka da Isra’ila, zuwa ta’addanci, kisan kiyashi, jefa su a cikin yunwa, da kashe jama’a, ya wuce duk wani mataki na lamirin dan adam,” in ji Sheikh Qassem.
Ya kuma yi kakkausar suka ga gazawar manyan kasashen duniya da gaza aiwatar da dokokin kasa da kasa, yana mai cewa, “Shiru da kasashen duniya suka yi, abin Allah wadai ne ga gwamnatocin kasashen duniya, musamman na kasashen musulmi da larabawa.
Da yake ishara da kiraye-kirayen baya-bayan nan da kasashe sama da ashirin suka yi na a dakatar da yakin, Sheikh Qassem ya yi ishara da cewa irin wadannan kalamai da cewa ba su isa ba ko kadan, Ya ce, “bai isa ba a ce kasashe 25 sun yi kira da a dakatar da yakin Gaza, wannan furucin kadai bai wadatar ba.
Sheikh Qassem ya yi kira da a kakaba takunkumi kan “Isra’ila”, da gurfanar da su a gaban shari’a, da kuma dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da ita.