Aminiya:
2025-06-14@02:02:27 GMT

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan ta’adda a Yobe

Published: 9th, June 2025 GMT

Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce ta kashe ’yan ta’adda da dama a cikin wasu jerin hare-hare na sama da na ƙasa da suka kai sansanonin ’yan ta’addan Boko Haram da ISWAP da ke Nzalgana, a ƙaramar hukumar Gujba ta Jihar Yobe a Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Sanarwar da rundunar ta wallafa a shafukanta na sada zumunta ta ce hare-haren da sojojin suka ƙaddamar da sanyin safiyar Litinin 9 ga watan Yuni sun yi sanadin mutuwar wani babban kwamandan Boko Haram a ƙauyukan Ngorgore da Malumti, Ameer Malam Jidda.

Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba Zaɓen 2027 ba — ACF NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba

Duk da cewa sanarwar ba ta yi ƙarin bayani game da jerin hare-haren ba, sai dai Zagazaola Makama, wani kwararren kan lamuran tsaron a yankin, ya ruwaito cewa sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK47 da harsasai da kuma babur daga hannun kwamandan da aka kashe.

Sai dai kuma sanarwar ta sojojin ta bayyana cewa sojojin sun sake samun ƙarin makamai da gawarwakin ‘yan ta’adda a Abadam bayan arangamar da suka yi da ‘yan ta’addan kwanan nan a Mallam Fatori.

Cikin ‘yan makonnin nan dai an yi ta samun rahotannin hare-haren da ‘yan ta’adda ke kai wa sansanonin sojoji a yankin.

Kazalika sojojin ƙasar su ma suna kai hare-hare ta sama kan sansanonin ‘yan ta’addan a yankin domin su hana su iya kai irin hare-haren da suke kai wa kan sojoji.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Jihar Yobe yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi karin haske game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarta a Kazakhstan, yana mai cewa, Sin na da yakininta hanyar taro, ita da sauran kasashen yankin tsakiyar Asiya biyar, za su zurfafa dunkulewa, da amincewa da juna, da gina matsaya guda ta fuskar hadin gwiwa, da zurfafa daidaiton dabarun ci gaba, da daga matsayin hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kara kuzarin gina al’umma mai makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya.

 

Bisa gayyatar da shugaban jamhuriyar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, tsakanin ranekun 16 zuwa 18 ga watan nan na Yuni. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI