Sojoji sun kashe kwamandan ’yan ta’adda a Yobe
Published: 9th, June 2025 GMT
Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce ta kashe ’yan ta’adda da dama a cikin wasu jerin hare-hare na sama da na ƙasa da suka kai sansanonin ’yan ta’addan Boko Haram da ISWAP da ke Nzalgana, a ƙaramar hukumar Gujba ta Jihar Yobe a Arewa maso Gabashin Nijeriya.
Sanarwar da rundunar ta wallafa a shafukanta na sada zumunta ta ce hare-haren da sojojin suka ƙaddamar da sanyin safiyar Litinin 9 ga watan Yuni sun yi sanadin mutuwar wani babban kwamandan Boko Haram a ƙauyukan Ngorgore da Malumti, Ameer Malam Jidda.
Duk da cewa sanarwar ba ta yi ƙarin bayani game da jerin hare-haren ba, sai dai Zagazaola Makama, wani kwararren kan lamuran tsaron a yankin, ya ruwaito cewa sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK47 da harsasai da kuma babur daga hannun kwamandan da aka kashe.
Sai dai kuma sanarwar ta sojojin ta bayyana cewa sojojin sun sake samun ƙarin makamai da gawarwakin ‘yan ta’adda a Abadam bayan arangamar da suka yi da ‘yan ta’addan kwanan nan a Mallam Fatori.
Cikin ‘yan makonnin nan dai an yi ta samun rahotannin hare-haren da ‘yan ta’adda ke kai wa sansanonin sojoji a yankin.
Kazalika sojojin ƙasar su ma suna kai hare-hare ta sama kan sansanonin ‘yan ta’addan a yankin domin su hana su iya kai irin hare-haren da suke kai wa kan sojoji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Jihar Yobe yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
An Jikkata Sojojin Sahayoniya 9 Ta Hanyar Take Su Da Mota
Kafafen watsa labarun HKI sun ce wani mutum a cikin motar da yake tukawa ya nufi kan ‘yan sahayoniya a mahadar “Hahsrun” a kusa da “Kafar-Yona”dake yammacin Tul-Karam.
Bayan da matumin ya take ‘yan sahayoniyar ya fice daga yankin ba tare an iya tsayar da shi ba.
Majiyar ta kara da cewa; 9 daga cikin ‘yan sahayoniyar da su ka jikkata sojoji ne.
Tashar talabijin din ta 12: ta ambaci cewa; Wanda ya take sojojin ya iya gudu daga wurin, ba tare da an tsayar da shi ba.
Ita kuwa jaridar ‘ Yasrael Home” ta bayyana cewa; An baza ‘yan sanda a wurin da aka kai hari, domin gano inda maharin yake.
Kungiyoyin Falasdinawa sun yi maraba da wannan harin, tare da yin kira a ci gaba da gudanar da irinsa da yawa.
Kungiyar Hamas ta ce, dole a tsammaci wannan irin harin, bisa la’akari da laifukan da HKI take tafkawa a Gaza da yammacin kogin Jordan.
Kungiyar Jihadul-Islami kuwa cewa ta yi, hari irin wannan yana kara tabbatar da yadda al’ummar Falasdinu ta sha alwashin ci gaba da riko da kasarta da kuma kalubalantar ‘yan mamaya da dukkanin abinda su ka mallaka.
Shi kuwa kwamitin gwagwarmaya na Falasdinu ta yi kira ne ga dukkanin Falasdinawa da su yunkura domin fada da sojojin sahayoniya.
Ita kuwa kungiyar “Mujahidun-al-Falasdiniyya ta sa wa harin albarka tare da bayyana shi a matsayin babban sako ga ‘yan mamaya dake cewa martani akan kisan gillar da suke yi zai fadada.