HausaTv:
2025-06-12@16:32:42 GMT

Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI

Published: 11th, June 2025 GMT

Sojojin kasar Yemen sun bada sanarwan kai hare-hare da makamai masu linzami kan tashar Jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv) a safiyar yau Laraba. Kuma makaman sun sami inda ake bukata.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa sojojin sun yi amfani da makamai masu linzami samfurin Bilistet a hare-haren, kuma sun kaisu ne tallafawa Falasdinawa a Gaza wadanda HKI takewa kissan kare dangi.

Labarin ya kara da cewa daya daga cikin makamai masu linzamin ya sami tashar jiragen kai tsaye ba tare da an kakkabishi ba.

Makaman sun hargitsa zirga-zirgan jiragen sama, a tasahr na wani lokaci sannan ya sa yahudawa tsakiyar Yafa (Telaviv) da yankin yamma da kogin Jordan da birnin Qudus shiga wurarenn fakewa.

Sannarda Burgediya Yahyah Saree ya bayyana ya kara jadda haramta sauka da tashin jiragen sama a tasahr sannan ya yi kira ga dukkan jiragen sama su dakatar da zuwa zuwa tashar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba

Wata mummunar guguwa ta yi sanadin mutuwar mutum shida sannan ta jikkata wasu 30 a garin Garba-Chede da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

A cewar wani mazaunin yankin wanda guguwar ta lalata wa gida mai suna Abubakar Dodo, an shafe shekaru masu yawa ba su ga irin ta ba a yankin saboda munin barnar da ta yi.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

A cewarsa, ban da gidaje, guguwar ta kuma lalata makarantu da masallatai da coci-coci, sannan kayan abinci na miliyoyin Naira sun salwanta.

Dagacin garin na Garba-Chede, Kaigama Maigandi, ya yi kira ga Gwamnan Jihar, Agbu Kefas, da ya taimaka wa mutanen yankin da iftila’in ya shafa domin su samu su gyara gidaje da wuraren kasuwancinsu.

A wani labarin kuma, wata tawagar wakilai daga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta ziyarci yankin domin jajanta musu da kuma ganin girman barnar domin ganin irin tallafin da za a yi musu.

Ayarin, wanda ke karkashin jagorancin Dr. Balutu Isa Mohammed, ya yi jaje ga mutanen tare da yi musu alkawarin ba su tallafin muhimman abubuwan da suke bukata domin su rage radadi.

Tawagar ta kuma ziyarci Dagacin garin tare da yi masa bayanin musabbabin zuwansu da kuma ayyukan da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
  • Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
  • Iran Ta Ce Wuraren Kai Farmaki A HKI Suna Hannu a Duka Sanda Ta Kawo hari Iran
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata
  • Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Gargadi Mahukuntan Taiwan Game Da Sayen Makamai Daga Amurka
  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza