Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
Published: 11th, June 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun bada sanarwan kai hare-hare da makamai masu linzami kan tashar Jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv) a safiyar yau Laraba. Kuma makaman sun sami inda ake bukata.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa sojojin sun yi amfani da makamai masu linzami samfurin Bilistet a hare-haren, kuma sun kaisu ne tallafawa Falasdinawa a Gaza wadanda HKI takewa kissan kare dangi.
Labarin ya kara da cewa daya daga cikin makamai masu linzamin ya sami tashar jiragen kai tsaye ba tare da an kakkabishi ba.
Makaman sun hargitsa zirga-zirgan jiragen sama, a tasahr na wani lokaci sannan ya sa yahudawa tsakiyar Yafa (Telaviv) da yankin yamma da kogin Jordan da birnin Qudus shiga wurarenn fakewa.
Sannarda Burgediya Yahyah Saree ya bayyana ya kara jadda haramta sauka da tashin jiragen sama a tasahr sannan ya yi kira ga dukkan jiragen sama su dakatar da zuwa zuwa tashar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen sama
এছাড়াও পড়ুন:
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA