Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya
Published: 10th, June 2025 GMT
Masu bayar da agajin gaggawa sun isa wurin jim kadan bayan karfe 9 na safe, inda hargitsi da firgici ya da baibaye mazauna harabar makarantar.
A cewar ‘yansandan yankin, dan bindigar ya shiga ajin karatun ne dauke da bindiga inda ya bude wuta kan mai uwa da wabi, sannan kuma ya harbe kansa.
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a Jihar Kano.
Aminiya ta gano yadda fashewar bam ɗin ya haddasa firgici a yankin da lamarin ya faru, inda jami’an tsaro da na agajin gaggawa suka garzaya wajen don kai ɗauki.
An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000 Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a FilatoKwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke yin jigilar ne wanda aka yi sakaci ya fashe.
“Na samu kiran gaggawa cewa wani abu mai tayar da hankali ya faru. Da na isa wajen, sai na ga abin kamar bama-baman sojoji ne suka fashe.
“Mutane 15 sun jikkata, kuma abin takaici, guda biyar sun rasu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa yankin domin samun kulawa ta gaggawa.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da kayan fashewar, wadda ta ke kan hanyar zuwa Jihar Yobe.
Har yanzu jami’an tsaro ba su tabbatar da ko motar sojoji ce ke ɗauke da kayan fashewar ba.
Rundunar na ci gaba da da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin da kuma abin da ya haddasa fashewar abun.
“Za mu samu cikakken bayani bayan kammala bincike,” in ji Kwamishinan.
Ya kuma roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu.
Ga hotunan yadda jami’an tsaro ke bincike kan lamarin: