Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baghae ya zargin gwamnatin Amurka da yin ba daidai ba saboda karin takunkuman tattalin arziki wanda ta dorawa kasar, wanda kuma yake nuna irin kiyayyar da takewa mutanen kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Esmael Baghae yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa bayan da hukumar baitul malin Amurka ta bayyana sunayen mutane 10 wadanda ta dorawa takunkuman tattalin arziki da kuma kamfanoni 27 mafi yawansu a hadaddiyar daulolin larabawa wato UAE.

Labarin ya kara da cewa wadan nan mutane suna taimakawa Iran a ayyukan Banki da jigilar manfetur a madadin Iraniyawa. Baghae ya bayyana wannan labarin a kan kariya kuma mummunan siyasar Amurka ce ga JMI.

Yace bayan haka wadan nan takunkuman basa bisa ka’idar doka kuma manufa it ace takurawa mutanen kasar Iran.

Sannan ya kammala da cewa wadan nan matakan zasu kara karfafa dauriyan mutanen kasar Iran ne kawai. Inji Baghe.

Sannan abin mamaki shi ne wadannan takunkuman suna zuwa ne a dai-dai lokacinda kasashen biyu suke tattaunawa kan shirin makamashin Nukliya na kasar. Wanda ya nuna cewa Amurka bata nufin alkhairi a tattaunawar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya

Shugaban kasar Iran Masuod Pezeshkiyan ya zanta ta wayar tarko tare da shugaban kasar Masar abdulfatta Assisi, inda suka taya juna murnar tahowar sallar Babba. Shugaban ya bayyana cewa kasar Iran tana da tsari ta makobta farko, don haka ne take, kara kyautata dangantaka da kasashe makobta da kuma musamman kasar ta Masar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a wata wayar tarho ta daban shugaban ya zanta da Yarima mai jiran gadon sarautan saudiya kuma Firay ministan kasar Muhammad bin Salman inda ya taya shi murnar zagayowar ranar Sallah babba sannan suka yi maganar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu. Duk tare da bambancin ra’ayin da kasashen biyu suke da shi dangane da yadda za’a warware matsalar falasdinawa kasashen biyu sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a gaza a kuma isar da kayakin agaji da gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Matakan Washington Na Hana ‘Yan Kasashen Musulmi Shiga  Amurka  Kiyayya Ce
  • Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Iran Ta Musanta Zargin Amurka Kan Cewa Kungiyoyi Masu Fada Ha HKI Suna Daukar Umurni Daga Wajenta Ne
  • Kotun ICC Ta Yi Tir Da Amurka Saboda Takunkuman Da Ta Dorawa Alkalan Kotun Don Hanata Aikinta Da Yenci
  • Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya